• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mambobin ASUU A Bauchi Sun Yi Zanga-zanga Kan Bukatunsu 

Sun Yi Tir Da Matakin Sayar Da Jami'o'i Da Fatali Da Tsarin IPPIS

by Khalid Idris Doya
4 months ago
in Manyan Labarai
0
ASUU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mambobin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), a Jihar Bauchi, sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Talata domin shaida wa duniya cewa har zuwa yanzu Gwamnatin tarayya ta kasa cimma bukatun da suke da su tare da neman yanayin koyarwa mai inganci.

Shiyyar ASUU na Bauchi ya kunshi jami’o’in Bauchi, Gombe, da jihar Filato sun yi zanga-zangar ne a Bauchi inda suka fito daga cikin jami’ar ATBU tare da fitowa kan titi na mintuna dauke da takardun da suke alamta bukatunsu daban-daban gami da yin wakokin neman goyon baya.

  • Jaruman Nollywood Da Kannywood Sun Yi Wa Jos Tsinke Don Mara Wa Tinubu Baya 
  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida, Shugaban kungiyar ASUU a jami’ar ATBU, Dakta Ibrahim Ibrahim Inuwa ya roki masu ruwa da tsaki a Nijeriya da su matsa wa Gwamnatin tarayya lamba wajen ganin ta cika dukkkanin bukatun Malaman jami’o’i domin tabbatar da ci gaban kasa da inganta harkokin ilimi.

Ya ce, dole ne su yi tsawa su yi tsayin daka wajen kare tsarin jami’o’i a kasar nan ta hanyar bin matakan da doka suka shimfida.

Kazalika, ASUU din ta yi tir gami da fatali da kokarin gwamnati na sayar da jami’o’in kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Mamayar Tattar 4

Tsokaci A Kan Mazajen Da Ke Bayyana Sirrukan Gidanjensu A Majalisa

Dakta Ibrahim ya ce tun lokacin da suka janye yajin aikin watanni 8 sakamakon umarnin kotu da bukatar wasu ‘yan Nijeriya, Gwamnatin tarayya take sako-sako da batun biya musu bukatunsu a maimakon haka ma sai biyansu albashin watan Oktoba ta yi ba yadda ya dace ba.

Ya kara da cewa da gangan wasu ke nacewa wajen maida jami’o’i zuwa masu zaman kansu domin wasu daidaiku ne ke amfana da jami’o’i masu zaman kansu kuma hakan ba zai taimaka wa talakawa kasa wajen samun ilimi cikin sauki ba.

ASUU ta kara da nuna damuwarta kan cewa bisa fito da tsarin biyan albashi ta IPPIS wasu hakkokinsu da dama da doka ya ware musu an danne musu kuma ba za su lamunce da hakan ba.

Kungiyar dai ya ce tana da tulin bukatun da suke son Gwamnatin tarayya ta cimma musu amma har yanzu yanzu ba su ga sakamakon mai kyau ba. Don haka ne suka nemi masu ruwa da tsaki da fa su sanya baki domin ganin an shawo kan matsalolin.

Har-ila-yau, sun ce basu son sake shiga yajin aiki a Nan kusa domin cigaban amsa amma ba za su zura ido Kuma ana zalumtaersu ba, don haka ne a cewarsu suka dauki matakin yin zanga-zanga domin nuna wa duniya cewa har yanzu yanzu Gwamnatin tarayya ba ta shirya wa kawo karshen matsalolin da malaman jami’o’i ke fama da su ba.

Tags: ASUUBauchiGwamnatin TarayyaIlimiTakaddamaYajin AikiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jaruman Nollywood Da Kannywood Sun Yi Wa Jos Tsinke Don Mara Wa Tinubu Baya 

Next Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Related

Tarihin Mamayar Tattar 4
Manyan Labarai

Tarihin Mamayar Tattar 4

1 day ago
Tsokaci A Kan Mazajen Da Ke Bayyana Sirrukan Gidanjensu A Majalisa
Manyan Labarai

Tsokaci A Kan Mazajen Da Ke Bayyana Sirrukan Gidanjensu A Majalisa

1 day ago
Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
Manyan Labarai

Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

2 days ago
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi
Manyan Labarai

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

2 days ago
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari
Manyan Labarai

Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

2 days ago
Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni
Manyan Labarai

Yadda Na’urar BBAS Ta Sauya Salon Zaben Gwamnoni

2 days ago
Next Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

LABARAI MASU NASABA

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.