ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mambobin ASUU A Bauchi Sun Yi Zanga-zanga Kan Bukatunsu 

Sun Yi Tir Da Matakin Sayar Da Jami'o'i Da Fatali Da Tsarin IPPIS

by Khalid Idris Doya
4 years ago
ASUU

Mambobin Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), a Jihar Bauchi, sun gudanar da zanga-zangar lumana a ranar Talata domin shaida wa duniya cewa har zuwa yanzu Gwamnatin tarayya ta kasa cimma bukatun da suke da su tare da neman yanayin koyarwa mai inganci.

Shiyyar ASUU na Bauchi ya kunshi jami’o’in Bauchi, Gombe, da jihar Filato sun yi zanga-zangar ne a Bauchi inda suka fito daga cikin jami’ar ATBU tare da fitowa kan titi na mintuna dauke da takardun da suke alamta bukatunsu daban-daban gami da yin wakokin neman goyon baya.

  • Jaruman Nollywood Da Kannywood Sun Yi Wa Jos Tsinke Don Mara Wa Tinubu Baya 
  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida, Shugaban kungiyar ASUU a jami’ar ATBU, Dakta Ibrahim Ibrahim Inuwa ya roki masu ruwa da tsaki a Nijeriya da su matsa wa Gwamnatin tarayya lamba wajen ganin ta cika dukkkanin bukatun Malaman jami’o’i domin tabbatar da ci gaban kasa da inganta harkokin ilimi.

ADVERTISEMENT

Ya ce, dole ne su yi tsawa su yi tsayin daka wajen kare tsarin jami’o’i a kasar nan ta hanyar bin matakan da doka suka shimfida.

Kazalika, ASUU din ta yi tir gami da fatali da kokarin gwamnati na sayar da jami’o’in kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Dakta Ibrahim ya ce tun lokacin da suka janye yajin aikin watanni 8 sakamakon umarnin kotu da bukatar wasu ‘yan Nijeriya, Gwamnatin tarayya take sako-sako da batun biya musu bukatunsu a maimakon haka ma sai biyansu albashin watan Oktoba ta yi ba yadda ya dace ba.

Ya kara da cewa da gangan wasu ke nacewa wajen maida jami’o’i zuwa masu zaman kansu domin wasu daidaiku ne ke amfana da jami’o’i masu zaman kansu kuma hakan ba zai taimaka wa talakawa kasa wajen samun ilimi cikin sauki ba.

ASUU ta kara da nuna damuwarta kan cewa bisa fito da tsarin biyan albashi ta IPPIS wasu hakkokinsu da dama da doka ya ware musu an danne musu kuma ba za su lamunce da hakan ba.

Kungiyar dai ya ce tana da tulin bukatun da suke son Gwamnatin tarayya ta cimma musu amma har yanzu yanzu ba su ga sakamakon mai kyau ba. Don haka ne suka nemi masu ruwa da tsaki da fa su sanya baki domin ganin an shawo kan matsalolin.

Har-ila-yau, sun ce basu son sake shiga yajin aiki a Nan kusa domin cigaban amsa amma ba za su zura ido Kuma ana zalumtaersu ba, don haka ne a cewarsu suka dauki matakin yin zanga-zanga domin nuna wa duniya cewa har yanzu yanzu Gwamnatin tarayya ba ta shirya wa kawo karshen matsalolin da malaman jami’o’i ke fama da su ba.

ASUU
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post

Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.