• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma 10, 000 Za Su Amfana Da Sabon Shirin Noman Rani A Sokoto

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Labarai
0
Manoma 10, 000 Za Su Amfana Da Sabon Shirin Noman Rani A Sokoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoma sama da dubu 10 ne za su ci moriyar sabon shirin bunkasa noman rani a Sokoto wanda aka bayar da aikinsa kan naira biliyan 3.4.

Shugaban Karamar Hukumar Kware, Honarabul Jafaru Hamza ne ya bayyana hakan a yau ga tawagar Kungiyar ‘Yan Jarida ta Kasa (NUJ) reshen Jihar Sakkwato a ziyarar gani da ido da suka kai a ayyukan da Gwamnatin Tambuwal ta aiwatar a Kware.

  • Na Yi Alkawarin Samar Da Wutar Lantarki Da Inganta Noman Rani – Atiku

“Wannan shirin wanda aikinsa ya kai kashi 90 cikin 100 zai bunkasa noman rani sosai, akalla sama da manoma 10, 000 za su ci moriya, aiki ne wanda zai habaka samar da abinci a ciki da wajen Jiha, haka ma zai bunkasa haraji da karuwar tattalin arziki.” Ya bayyana.

Honarabul Jafaru wanda ya bayyana cewar shirin bunkasa noman rani na Kware da za a kammala a Disamba, hadakar shiri ne tsakanin Gwamnatin Sakkwato, Gwamnatin Tarayya da kuma Bankin Bunkasa Kasashen Afrika, ya ce shirin zai rika samar da shinkafa ga sabon kamfanin Shinkafa na Dangote da za a kammala a Karamar Hukumar.

Ya ce tun zamanin Firmiyan Yankin Arewa, Sa Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato aka assasa shirin noman rani a Kware amma sama da shekaru 30 wajen ba ya aiki, wanda akan hakan ne Gwamnatin Tambuwal ta yi hobbasar kwazon raya aikin noma a wajen.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ya ce a yanzu haka an gyara kadada 450 cikin 800 da ke akwai, haka ma za su rika samun ruwa ne daga tafkin Rima da na Kalmalo, haka ma an dauki kwararan matakan kiyaye ambaliyar ruwa.

Shugaban wanda ya zagaya da ‘yan Kungiyar a wuraren mabambantan ayyuka ya bayyana cewar “Kun ga sabuwar Babbar Asibitin Kware wadda aka bude a shekarar da ta gabata kuma ta na aiki yadda ya kamata, kun kuma ga sabon gidan ruwa mai daukar lita miliyan 1.5 da sabon ofishin ‘yan Sanda da makarantu, hanyoyin mota da sauransu. Bakidaya Gwamnatin Tambuwal daga 2015 zuwa yau ta aiwatar da ayyuka sama da 200 a Kware wadanda suka yi matukar tasiri ga al’umma.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Harba kuKmbon Shenzhou-15 Dauke Da ‘Yan Sama Jannati 3

Next Post

Jihar Kebbi Zata Samu Tallafin Dala 350,000 – ECOWAS 

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

9 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

9 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

10 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

10 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

13 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

14 hours ago
Next Post
Jihar Kebbi Zata Samu Tallafin Dala 350,000 – ECOWAS 

Jihar Kebbi Zata Samu Tallafin Dala 350,000 - ECOWAS 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.