• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasashen Duniya Na Neman Cin Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan mako ne ministan harkokin wajen kasar Italiya Antonio Tajani ya fara ziyara a kasar Sin. Ziyarar da ta zo a daidai lokacin da ake ta tsokaci game da kasancewar kasar cikin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, kasancewarta kasar Turai tilo dake cikin shawarar.

Yayin da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ke cika shekaru 10, kasar Italiya ta kasance cikin wadanda suka ci gajiyarta. Misali kadan daga ciki ya hada da yadda yawan cinikayya tsakanin kasashen biyu ya habaka zuwa kusan dala biliyan 80 daga dala biliyan 50.

  • Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

Haka kuma yawan kayayyakin da Italiya ke shigo da su kasar Sin ya karu da kaso 30 cikin shekaru 5 da suka gabata. Wannan kadai ya nuna yadda Sin take taka gagarumar rawa wajen bunkasa cinikayya da ma tattalin arzikin kasar ta Turai. Haka zalika, ya nuna cewa, duk da yunkurin da wasu kasashen yamma ke yi na neman raba gari da Sin ko rage dogaro da ita, ra’ayin wasu da dama ya bambanta, kuma sun san abun da kasashensu da duniya ke bukata domin samun ci gaba a wannan zamani da ake fuskantar kalubale. Za mu iya gane hakan idan muka yi la’akari da cewa, Antonio Tajani shi ne babban jami’i na 4 daga kasashen kungiyar G7 da ya kawo ziyara Sin a baya-bayan nan.

Irin wannan ziyara da manyan jami’an manyan kasashe ke kawowa kasar Sin, yana kara bayyanawa al’ummar duniya cewa, jita-jitar da ake yadawa ba su da kamshin gaskiya ko kadan, kana ana yinsu ne da zummar bata sunan kasar Sin da kuma kokarin dakile ci gabanta, ganin irin tagomashin da take samu a duniya da ma jajircewarta wajen raya kanta bisa tsayawa da kafarta.

A yayin tattaunawarsa da ’yan kasuwar kasarsa dake Sin, Tajani ya ce gwamnatinsu na son inganta musu hanyoyin kara shiga kasuwar kasar Sin. Abun nufi, gwamnatin kasarsa na son kara cin gajiyar kasar Sin da ma dimbin damarmakin kasuwanci da bude kofar da take kara yi ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na kasashen ketare. Lamarin dake kara jaddada cewa, raba gari da kasar Sin ba abu ne mai yiwuwa ba. Kana su ma manyan kasashen duniya, suna son cin gajiyar ci gaban kasar Sin da dimbin damarmakin da take da su.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Ita dai Sin ta sha nanata cewa, a shirye take ta yayata fasahohinta tare da ba kasashen duniya damar cin gajiyar ci gabanta da tafarkin da ta dauka na zamanintar da kanta. (Faeza Mustapha)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

Related

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

1 hour ago
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

2 hours ago
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari
Daga Birnin Sin

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

3 hours ago
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

5 hours ago
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

5 hours ago
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu
Daga Birnin Sin

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

6 hours ago
Next Post
Red Cross

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.