ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasashen Duniya Na Neman Cin Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A farkon wannan mako ne ministan harkokin wajen kasar Italiya Antonio Tajani ya fara ziyara a kasar Sin. Ziyarar da ta zo a daidai lokacin da ake ta tsokaci game da kasancewar kasar cikin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, kasancewarta kasar Turai tilo dake cikin shawarar.

Yayin da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ke cika shekaru 10, kasar Italiya ta kasance cikin wadanda suka ci gajiyarta. Misali kadan daga ciki ya hada da yadda yawan cinikayya tsakanin kasashen biyu ya habaka zuwa kusan dala biliyan 80 daga dala biliyan 50.

  • Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

Haka kuma yawan kayayyakin da Italiya ke shigo da su kasar Sin ya karu da kaso 30 cikin shekaru 5 da suka gabata. Wannan kadai ya nuna yadda Sin take taka gagarumar rawa wajen bunkasa cinikayya da ma tattalin arzikin kasar ta Turai. Haka zalika, ya nuna cewa, duk da yunkurin da wasu kasashen yamma ke yi na neman raba gari da Sin ko rage dogaro da ita, ra’ayin wasu da dama ya bambanta, kuma sun san abun da kasashensu da duniya ke bukata domin samun ci gaba a wannan zamani da ake fuskantar kalubale. Za mu iya gane hakan idan muka yi la’akari da cewa, Antonio Tajani shi ne babban jami’i na 4 daga kasashen kungiyar G7 da ya kawo ziyara Sin a baya-bayan nan.

ADVERTISEMENT

Irin wannan ziyara da manyan jami’an manyan kasashe ke kawowa kasar Sin, yana kara bayyanawa al’ummar duniya cewa, jita-jitar da ake yadawa ba su da kamshin gaskiya ko kadan, kana ana yinsu ne da zummar bata sunan kasar Sin da kuma kokarin dakile ci gabanta, ganin irin tagomashin da take samu a duniya da ma jajircewarta wajen raya kanta bisa tsayawa da kafarta.

A yayin tattaunawarsa da ’yan kasuwar kasarsa dake Sin, Tajani ya ce gwamnatinsu na son inganta musu hanyoyin kara shiga kasuwar kasar Sin. Abun nufi, gwamnatin kasarsa na son kara cin gajiyar kasar Sin da ma dimbin damarmakin kasuwanci da bude kofar da take kara yi ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na kasashen ketare. Lamarin dake kara jaddada cewa, raba gari da kasar Sin ba abu ne mai yiwuwa ba. Kana su ma manyan kasashen duniya, suna son cin gajiyar ci gaban kasar Sin da dimbin damarmakin da take da su.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Ita dai Sin ta sha nanata cewa, a shirye take ta yayata fasahohinta tare da ba kasashen duniya damar cin gajiyar ci gabanta da tafarkin da ta dauka na zamanintar da kanta. (Faeza Mustapha)

 

 

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Red Cross

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.