• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

by Khalid Idris Doya
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin haɗakar (JAC) na ƙungiyar malamai da waɗanda ba malamai ba na manyan makarantu mallakin gwamnatin jihar Bauchi sun shelanta tafiya yajin aikin sai babaa ta gani wanda hakan zai kai ga kulle makarantu baki ɗaya bisa rashin aiwatar musu da sabon tsarin biyan albashi na dukkanin ma’aikatan manyan makarantu wato (CONPCASS da CONTEDISS).

Shugaban kwamitin JAC, Kwamared Abubakar Ahmed wanda ya karanta jawabin bayan taron gaggawa da suka gudanar a ofishin ASUP da ke kwalejin ATAP ranar Litinin, ya ce, yajin aikin zai kai har a kulle makarantun dukka zai fara ne daga ranar Alhamis 2 ga watan Janairun 2025.

  • NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi
  • Kirsimeti: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 15 Da Ake Zargi Da Laifin Sata A Bauchi

A cewarsa, sun ɗauki wannan matsayar ne biyo bayan rashin gamsuwa da irin amsar da suka samu daga wakilan gwamnatin jihar da kuma irin nuna rashin damuwa da suka yi da buƙatun ƙungiyar a yayin zaman sulhu da suka yi a tare.

Kwamared Abubakar ya ce sun kuma cimma matsayar ne bayan ƙarewar wa’adin mako biyu da suka bayar wa gwamanti na yajin aikin gargaɗi da suka yi daga ranar 16 zuwa 30 na watan Disamban 2024 ba tare da samun wani sakamakon mai kyau daga wakilan gwamnati ba.

Makarantu

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Makarantun da suke ƙarƙashin JAC ɗin sun haɗa da kwalejin kimiyya da fasaha ta Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Bauchi da kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa, Kangere da Kwalejin ilimi da nazarin ilimin Shari’a da karatun komai da ruwanka ta A.D Rufai da ke Misau da kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare da kwalejin ilimin harkokin noma da ke Bauchi da kwalejin horas da nasu da ungomaza ta Bill and Melinda Gates da ke Ningi.

Kwamitin ya nuna damuwarsa kan yadda wakilan da gwamnatin ta turo suke ƙoƙarin kawo naƙasu ga azamar gwamnan jihar na kyautata harkokin ilimi a manyan makarantun jihar, inda suka nemi a gaggauta aiwatar da sabon tsarin albashi kamar yadda yake ƙunshe a tsarin CONPCASS da CONTEDISS.

Injiniya Abubakar Ahmed ya nuna damuwa kan yadda ake barazana ga jagororin JAC da mambobinsu a faɗin makarantun bisa yadda suke tsayuwar daka wajen ganin an biya musu buƙatunsu. Sai ya nemi iyaye da dalibai da su yi haƙuri da zarar komai ya daidaita za su koma bakin aikinsu yadda ya kamata.

Makarantu

Kana sun yi kira ga gwamnatin jihar Bauchi Bala Muhammad da ya tashi tsaye ya bibiyi lamarin domin gudun janyo naƙasu ga harkokin ilimi da kuma nazartar matakan da wakilan gwamnati ke ɗauka wanda ƙungiyar ta ce sam ba za su taimaka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiSchool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Farko Kan Bincike Da Aikace-Aikacen Tashar Sararin Samaniya

Next Post

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

1 hour ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

8 hours ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

8 hours ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

1 day ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

1 day ago
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

2 days ago
Next Post
Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.