ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Makarantu

Kwamitin haɗakar (JAC) na ƙungiyar malamai da waɗanda ba malamai ba na manyan makarantu mallakin gwamnatin jihar Bauchi sun shelanta tafiya yajin aikin sai babaa ta gani wanda hakan zai kai ga kulle makarantu baki ɗaya bisa rashin aiwatar musu da sabon tsarin biyan albashi na dukkanin ma’aikatan manyan makarantu wato (CONPCASS da CONTEDISS).

Shugaban kwamitin JAC, Kwamared Abubakar Ahmed wanda ya karanta jawabin bayan taron gaggawa da suka gudanar a ofishin ASUP da ke kwalejin ATAP ranar Litinin, ya ce, yajin aikin zai kai har a kulle makarantun dukka zai fara ne daga ranar Alhamis 2 ga watan Janairun 2025.

  • NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi
  • Kirsimeti: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 15 Da Ake Zargi Da Laifin Sata A Bauchi

A cewarsa, sun ɗauki wannan matsayar ne biyo bayan rashin gamsuwa da irin amsar da suka samu daga wakilan gwamnatin jihar da kuma irin nuna rashin damuwa da suka yi da buƙatun ƙungiyar a yayin zaman sulhu da suka yi a tare.

ADVERTISEMENT

Kwamared Abubakar ya ce sun kuma cimma matsayar ne bayan ƙarewar wa’adin mako biyu da suka bayar wa gwamanti na yajin aikin gargaɗi da suka yi daga ranar 16 zuwa 30 na watan Disamban 2024 ba tare da samun wani sakamakon mai kyau daga wakilan gwamnati ba.

Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Makarantun da suke ƙarƙashin JAC ɗin sun haɗa da kwalejin kimiyya da fasaha ta Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Bauchi da kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa, Kangere da Kwalejin ilimi da nazarin ilimin Shari’a da karatun komai da ruwanka ta A.D Rufai da ke Misau da kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare da kwalejin ilimin harkokin noma da ke Bauchi da kwalejin horas da nasu da ungomaza ta Bill and Melinda Gates da ke Ningi.

Kwamitin ya nuna damuwarsa kan yadda wakilan da gwamnatin ta turo suke ƙoƙarin kawo naƙasu ga azamar gwamnan jihar na kyautata harkokin ilimi a manyan makarantun jihar, inda suka nemi a gaggauta aiwatar da sabon tsarin albashi kamar yadda yake ƙunshe a tsarin CONPCASS da CONTEDISS.

Injiniya Abubakar Ahmed ya nuna damuwa kan yadda ake barazana ga jagororin JAC da mambobinsu a faɗin makarantun bisa yadda suke tsayuwar daka wajen ganin an biya musu buƙatunsu. Sai ya nemi iyaye da dalibai da su yi haƙuri da zarar komai ya daidaita za su koma bakin aikinsu yadda ya kamata.

Makarantu

Kana sun yi kira ga gwamnatin jihar Bauchi Bala Muhammad da ya tashi tsaye ya bibiyi lamarin domin gudun janyo naƙasu ga harkokin ilimi da kuma nazartar matakan da wakilan gwamnati ke ɗauka wanda ƙungiyar ta ce sam ba za su taimaka ba.

Makarantu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.