ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Makarantu

Kwamitin haɗakar (JAC) na ƙungiyar malamai da waɗanda ba malamai ba na manyan makarantu mallakin gwamnatin jihar Bauchi sun shelanta tafiya yajin aikin sai babaa ta gani wanda hakan zai kai ga kulle makarantu baki ɗaya bisa rashin aiwatar musu da sabon tsarin biyan albashi na dukkanin ma’aikatan manyan makarantu wato (CONPCASS da CONTEDISS).

Shugaban kwamitin JAC, Kwamared Abubakar Ahmed wanda ya karanta jawabin bayan taron gaggawa da suka gudanar a ofishin ASUP da ke kwalejin ATAP ranar Litinin, ya ce, yajin aikin zai kai har a kulle makarantun dukka zai fara ne daga ranar Alhamis 2 ga watan Janairun 2025.

  • NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi
  • Kirsimeti: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 15 Da Ake Zargi Da Laifin Sata A Bauchi

A cewarsa, sun ɗauki wannan matsayar ne biyo bayan rashin gamsuwa da irin amsar da suka samu daga wakilan gwamnatin jihar da kuma irin nuna rashin damuwa da suka yi da buƙatun ƙungiyar a yayin zaman sulhu da suka yi a tare.

ADVERTISEMENT

Kwamared Abubakar ya ce sun kuma cimma matsayar ne bayan ƙarewar wa’adin mako biyu da suka bayar wa gwamanti na yajin aikin gargaɗi da suka yi daga ranar 16 zuwa 30 na watan Disamban 2024 ba tare da samun wani sakamakon mai kyau daga wakilan gwamnati ba.

Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Makarantun da suke ƙarƙashin JAC ɗin sun haɗa da kwalejin kimiyya da fasaha ta Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Bauchi da kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa, Kangere da Kwalejin ilimi da nazarin ilimin Shari’a da karatun komai da ruwanka ta A.D Rufai da ke Misau da kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare da kwalejin ilimin harkokin noma da ke Bauchi da kwalejin horas da nasu da ungomaza ta Bill and Melinda Gates da ke Ningi.

Kwamitin ya nuna damuwarsa kan yadda wakilan da gwamnatin ta turo suke ƙoƙarin kawo naƙasu ga azamar gwamnan jihar na kyautata harkokin ilimi a manyan makarantun jihar, inda suka nemi a gaggauta aiwatar da sabon tsarin albashi kamar yadda yake ƙunshe a tsarin CONPCASS da CONTEDISS.

Injiniya Abubakar Ahmed ya nuna damuwa kan yadda ake barazana ga jagororin JAC da mambobinsu a faɗin makarantun bisa yadda suke tsayuwar daka wajen ganin an biya musu buƙatunsu. Sai ya nemi iyaye da dalibai da su yi haƙuri da zarar komai ya daidaita za su koma bakin aikinsu yadda ya kamata.

Makarantu

Kana sun yi kira ga gwamnatin jihar Bauchi Bala Muhammad da ya tashi tsaye ya bibiyi lamarin domin gudun janyo naƙasu ga harkokin ilimi da kuma nazartar matakan da wakilan gwamnati ke ɗauka wanda ƙungiyar ta ce sam ba za su taimaka ba.

Makarantu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Next Post
Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.