ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marwa Ya Kara Samun Lambar Yabo

by Leadership Hausa
3 years ago
Marwa

A karo na biyar a cikin watanni biyu, shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA), Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya) ya samu karin lambar yabo.

Idan ba a manta ba dai a watan da ta gabata, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karrama Marwa sau biyu, inda ya ba shi lambar yabo ta kasa matakin CON, kazalika, kuma ya kara karrama shi bayan mako guda da lambar yabo bisa bajintar da ya nuna a yaki da miyagun kwayoyi.

  • Buhari Ya Taya Jonathan Murnar Cika Shekaru 65 
  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3) Wakokin Daular Tang

Biyo bayan wadannan karramawar ne, kungiyar al’umman garin Michika na Jihar Adamawa suka yi taro na musamman, inda suka karrama Marwa a matsayin dansu da ya nuna bajinta na musamman a Nijeriya. Kungiyar ta karrama shi ne tare da wasu fitattun ‘yan garin na Michika.

ADVERTISEMENT

Babu shakka bajintar Marwa na inganta yaki da ta’amuli da miyagun kwayoyi abu ne da ya bayyana, lura da nasarori da hukumar NDLEA take samu a kullum. Ko a yau, hukumar ta fitar da sanarwar kama sama da tan bakwai na wiwi wanda yawan sa ya haura kilogiram dubu bakawai.

Alkaluman bayanai sun yi nuni da cewa, hukumar NDLEA ta kama sama da mutane 8,996 a cikin shekarar 2022. A bangaren kayan maye kuma, hukumar ta kama sama da kilogiram 219,576 na miyagun kwayoyi a wurare daban-daban a Nijeriya a cikin shekarar nan. Kazalika, hukumar ta lalata gonakin wiwi wanda yawan su ya kai hekta 324. Haka ma hukumar ta yi nasarar gyara tunanin (rehabilitation) na mashaya 6,244 a cikin shekarar nan.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

A kwanan nan ne hukumar ta yi shahararren kamun nan da ta yi na hodar iblis wanda yawansa ya kai tan 1.8 a wani gidan ajiya a Jihar Legas. Hodar iblis din wanda aka kiyasta kudinsa ya kai Naira biliyan 194, ya kasance kamu mafi girma na hodar iblis da hukumar ta yi a lokaci daya tun bayan kafa hukumar a shekaru 30 da suka wuce.

Adadin nasarorin da Marwa ya samu a yayin shugabancin hukumar NDLEA ba za su kirgu ba. Kuma wannan ba shi ne karshe ba, saboda har yanzu bakin alkalami a jike yake da tawadar rubuta nasarori da hukumar take ci gaba da samu a yaki da fataucin miyagun kwayoyi.

Idan akwai abun da Marwa ya nuna wa duniya da ya kamata na baya su yi koyi da shi, to ba zai wuce tsayuwa da gaske wajen aiwatar da aiki a duk inda ya samu kansa ba. Za a gane hakan idan aka waiwaya zuwa mukaman da ya rike a baya, kamar na gwamnan Jihar Legas da makamantansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

Shugaba Buhari Zai Kaddamar Da Aikin Tono Man Fetur A Jihohin Bauchi Da Gombe

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.