• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana tattalin arziki sun yi kira ga gwamnati da ta rage harajin da ake dora wa   kananan masana’antu domin su samu damar biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da gwamnati ta cimm a yarjejniyar ta da kungiyar kwadago a kwanan nan.

 

Farfesa Akpan Ekpo, malami a jami’ar Uyo, ya bayyana haka a tattaunawarsa da manema labarai a ranar Litinin.

  • Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Ya kara da cewa, ya kamata a tsame manyan kamfanonin da suke da karfin biya wannan sabon mafi karancin albashi daga wannan tsari na rage haraji.

 

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Ya lura da cewa, hanya mafi sauki da gwamnati za ta taimaka wa bangaren kamfanoni masu zaman kansu daba za su iya biyan mafi karancin albashi ba shi ne na rage musu haraji.

 

“Saukin da kananan masana’antu za su samu shi ne na rage musu haraji domin yana da wahala a ce gwamnati za ta basu wani tallafi na kudi, amma yana da matukara sauki a rage musu haraji na wani lokaci,” in ji masananin tattalin arzikin.

 

Ya kuma bayar da hujjar cewa, a halin yanzu masu kananan masana’antu na fuskatar matsaloli da dama ciki har da na rashin daidaiton kudaden kasashen waje da rashin tsayayyen wutar lantarki.

 

Ya ce, in har ba a samu bayar da wannan tallafin ba akwai yiwuwar a samu rashin ayyukan yi da karin marasa ayyuka a kasa saboda za a iya koran ma’aikata a daga bakin aikinsu.

 

Haka kuma wani masanin tattalin arziki mai suna Mista Dr Muda Yusuf, a tattaunawarsa da manema labarai ya amince da matsayar Farfesan ya kuma ce, yanayin da ake ciki a halin yanzu baya taimaka wa bangaren masu masana’antu masu zaman kansu a Nijeriya a saboda haka ya bukaci gwamnati ta samar da hanyoyin taimakawa masa’anantu domin su samu cimma biya wannan mafi karancin albashin.

 

Idan za a iya tunawa, kungiyar masu masana’atu ta Nijeriya ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta cika alkawarinta na tallafa wa masa’antu masu zaman kansu domin su iya biyan mafi karancin albashi na 70,000 da aka cimma da kungiyar kwadago a kasar nan.

 

Shugaban kungiyar, Segun Ajayi-Kadir ya yi wannan kiran ga gwamnatin inda ya ce wannan ne hanya mafi sauki da gwamnati za ta cika alkawarin ta.

A ranar 18 ga watan Yuli ne Shugaba Tinubu ya amince da Naira 70,000 matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiTabarbarewar tattalin arzikin NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta

Next Post

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

4 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

2 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.