• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana tattalin arziki sun yi kira ga gwamnati da ta rage harajin da ake dora wa   kananan masana’antu domin su samu damar biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da gwamnati ta cimm a yarjejniyar ta da kungiyar kwadago a kwanan nan.

 

Farfesa Akpan Ekpo, malami a jami’ar Uyo, ya bayyana haka a tattaunawarsa da manema labarai a ranar Litinin.

  • Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Ya kara da cewa, ya kamata a tsame manyan kamfanonin da suke da karfin biya wannan sabon mafi karancin albashi daga wannan tsari na rage haraji.

 

Labarai Masu Nasaba

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Ya lura da cewa, hanya mafi sauki da gwamnati za ta taimaka wa bangaren kamfanoni masu zaman kansu daba za su iya biyan mafi karancin albashi ba shi ne na rage musu haraji.

 

“Saukin da kananan masana’antu za su samu shi ne na rage musu haraji domin yana da wahala a ce gwamnati za ta basu wani tallafi na kudi, amma yana da matukara sauki a rage musu haraji na wani lokaci,” in ji masananin tattalin arzikin.

 

Ya kuma bayar da hujjar cewa, a halin yanzu masu kananan masana’antu na fuskatar matsaloli da dama ciki har da na rashin daidaiton kudaden kasashen waje da rashin tsayayyen wutar lantarki.

 

Ya ce, in har ba a samu bayar da wannan tallafin ba akwai yiwuwar a samu rashin ayyukan yi da karin marasa ayyuka a kasa saboda za a iya koran ma’aikata a daga bakin aikinsu.

 

Haka kuma wani masanin tattalin arziki mai suna Mista Dr Muda Yusuf, a tattaunawarsa da manema labarai ya amince da matsayar Farfesan ya kuma ce, yanayin da ake ciki a halin yanzu baya taimaka wa bangaren masu masana’antu masu zaman kansu a Nijeriya a saboda haka ya bukaci gwamnati ta samar da hanyoyin taimakawa masa’anantu domin su samu cimma biya wannan mafi karancin albashin.

 

Idan za a iya tunawa, kungiyar masu masana’atu ta Nijeriya ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta cika alkawarinta na tallafa wa masa’antu masu zaman kansu domin su iya biyan mafi karancin albashi na 70,000 da aka cimma da kungiyar kwadago a kasar nan.

 

Shugaban kungiyar, Segun Ajayi-Kadir ya yi wannan kiran ga gwamnatin inda ya ce wannan ne hanya mafi sauki da gwamnati za ta cika alkawarin ta.

A ranar 18 ga watan Yuli ne Shugaba Tinubu ya amince da Naira 70,000 matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiTabarbarewar tattalin arzikin NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta

Next Post

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Related

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

2 days ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

2 days ago
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

2 days ago
Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

1 week ago
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
Tattalin Arziki

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

1 week ago
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

2 weeks ago
Next Post
Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.