• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji

by Bello Hamza
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Masana Sun Nemi Gwamnati Ta Rage Wa Kananan Masana’antu Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana tattalin arziki sun yi kira ga gwamnati da ta rage harajin da ake dora wa   kananan masana’antu domin su samu damar biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da gwamnati ta cimm a yarjejniyar ta da kungiyar kwadago a kwanan nan.

 

Farfesa Akpan Ekpo, malami a jami’ar Uyo, ya bayyana haka a tattaunawarsa da manema labarai a ranar Litinin.

  • Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta
  • Ƴancin Gashin Kai: Gwamnati Ta Gargadi Ƙananan Hukumomi Kan Kashe Kuɗaɗensu

Ya kara da cewa, ya kamata a tsame manyan kamfanonin da suke da karfin biya wannan sabon mafi karancin albashi daga wannan tsari na rage haraji.

 

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Ya lura da cewa, hanya mafi sauki da gwamnati za ta taimaka wa bangaren kamfanoni masu zaman kansu daba za su iya biyan mafi karancin albashi ba shi ne na rage musu haraji.

 

“Saukin da kananan masana’antu za su samu shi ne na rage musu haraji domin yana da wahala a ce gwamnati za ta basu wani tallafi na kudi, amma yana da matukara sauki a rage musu haraji na wani lokaci,” in ji masananin tattalin arzikin.

 

Ya kuma bayar da hujjar cewa, a halin yanzu masu kananan masana’antu na fuskatar matsaloli da dama ciki har da na rashin daidaiton kudaden kasashen waje da rashin tsayayyen wutar lantarki.

 

Ya ce, in har ba a samu bayar da wannan tallafin ba akwai yiwuwar a samu rashin ayyukan yi da karin marasa ayyuka a kasa saboda za a iya koran ma’aikata a daga bakin aikinsu.

 

Haka kuma wani masanin tattalin arziki mai suna Mista Dr Muda Yusuf, a tattaunawarsa da manema labarai ya amince da matsayar Farfesan ya kuma ce, yanayin da ake ciki a halin yanzu baya taimaka wa bangaren masu masana’antu masu zaman kansu a Nijeriya a saboda haka ya bukaci gwamnati ta samar da hanyoyin taimakawa masa’anantu domin su samu cimma biya wannan mafi karancin albashin.

 

Idan za a iya tunawa, kungiyar masu masana’atu ta Nijeriya ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta cika alkawarinta na tallafa wa masa’antu masu zaman kansu domin su iya biyan mafi karancin albashi na 70,000 da aka cimma da kungiyar kwadago a kasar nan.

 

Shugaban kungiyar, Segun Ajayi-Kadir ya yi wannan kiran ga gwamnatin inda ya ce wannan ne hanya mafi sauki da gwamnati za ta cika alkawarin ta.

A ranar 18 ga watan Yuli ne Shugaba Tinubu ya amince da Naira 70,000 matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiTabarbarewar tattalin arzikin NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester City Na Buƙatar Yuro Miliyan 77 Kafin A Ɗauki Ɗan Wasan Gabanta

Next Post

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

2 weeks ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

3 weeks ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

4 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 months ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 months ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 months ago
Next Post
Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

Rundunar ‘Yansandan Kano Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Laifin Kisan Kai Bayan Shekara 6

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.