• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

by Sulaiman
3 weeks ago
GGI

A kwanan nan ne sashen watsa shirye-shirye a yankunan Asiya da Afirka na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG), tare da hadin gwiwar ofisoshin jakadancin kasar Sin da ke wasu kasashe, da cibiyoyin nazari na wurin, suka shirya wasu tarukan kara wa juna sani a kasashen Pakistan, Philippines, Cambodia, Laos, Kenya, da Turkiya, game da shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da kasar Sin ta gabatar.

Jami’ai, masana da wakilan kafafen yada labarai sun ce, shawarar ta gabatar da yadda za a cike “gibin jagoranci” na duniya tare da samar da ingantaccen tsari don magance babakeren bangare guda, da karfafa fada-a-jin kasashe masu tasowa da samar da tsarin kasa da kasa mafi adalci.

Shahararren masani kan harkokin kasa da kasa na kasar Kenya Cavince Adhere, ya yi imanin cewa, wasu hukumomi da cibiyoyi na kasa da kasa sun dade a karkashin ikon wasu kasashe, kuma galibi ana yin watsi da muryoyin kasashe masu tasowa. A yayin da ake fama da “gibin jagorancin” duniya, al’ummomin kasa da kasa na bukatar mafita ta gaskiya da adalci cikin gaggawa. Gabatar da shawarar inganta jagorancin duniya “ta dace da buri na bai daya na duk jama’ar kasashe kuma tana kunshe da biyan bukatun harkokin duniyar yau cikin gaggawa.”

Shi ma da yake bayani a wajen taron, Patrick Maluki, shugaban tsangayar nazarin harkokin waje ta jami’ar Nairobi ta Kenya, ya bayyana cewa, shawarar da Xi Jinping ya gabatar ta samar da wani sabon dandali ga kasashen Afirka na shiga harkokin kasa da kasa da samun ci gaba mai dorewa. Ya ce, “A tarihi, an dade ana mayar da Afirka saniyar ware. Muhimman ra’ayoyin da ke cikin shawarar sun yi daidai da bukatun ci gaban Afirka. Ya kamata kasashen Afirka na yau su zama masu shiga a dama da su sosai a harkokin jagorancin duniya.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
Daga Birnin Sin

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Next Post
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.