• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

by Sulaiman
2 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan ne sashen watsa shirye-shirye a yankunan Asiya da Afirka na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG), tare da hadin gwiwar ofisoshin jakadancin kasar Sin da ke wasu kasashe, da cibiyoyin nazari na wurin, suka shirya wasu tarukan kara wa juna sani a kasashen Pakistan, Philippines, Cambodia, Laos, Kenya, da Turkiya, game da shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da kasar Sin ta gabatar.

Jami’ai, masana da wakilan kafafen yada labarai sun ce, shawarar ta gabatar da yadda za a cike “gibin jagoranci” na duniya tare da samar da ingantaccen tsari don magance babakeren bangare guda, da karfafa fada-a-jin kasashe masu tasowa da samar da tsarin kasa da kasa mafi adalci.

Shahararren masani kan harkokin kasa da kasa na kasar Kenya Cavince Adhere, ya yi imanin cewa, wasu hukumomi da cibiyoyi na kasa da kasa sun dade a karkashin ikon wasu kasashe, kuma galibi ana yin watsi da muryoyin kasashe masu tasowa. A yayin da ake fama da “gibin jagorancin” duniya, al’ummomin kasa da kasa na bukatar mafita ta gaskiya da adalci cikin gaggawa. Gabatar da shawarar inganta jagorancin duniya “ta dace da buri na bai daya na duk jama’ar kasashe kuma tana kunshe da biyan bukatun harkokin duniyar yau cikin gaggawa.”

Shi ma da yake bayani a wajen taron, Patrick Maluki, shugaban tsangayar nazarin harkokin waje ta jami’ar Nairobi ta Kenya, ya bayyana cewa, shawarar da Xi Jinping ya gabatar ta samar da wani sabon dandali ga kasashen Afirka na shiga harkokin kasa da kasa da samun ci gaba mai dorewa. Ya ce, “A tarihi, an dade ana mayar da Afirka saniyar ware. Muhimman ra’ayoyin da ke cikin shawarar sun yi daidai da bukatun ci gaban Afirka. Ya kamata kasashen Afirka na yau su zama masu shiga a dama da su sosai a harkokin jagorancin duniya.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Labarai Masu Nasaba

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI

Next Post

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Related

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

51 minutes ago
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

3 hours ago
Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori

4 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

5 hours ago
Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO
Daga Birnin Sin

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

23 hours ago
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

1 day ago
Next Post
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

LABARAI MASU NASABA

GGI

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

September 21, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

September 21, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

September 21, 2025
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

September 21, 2025
Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

September 21, 2025
arewa

Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI

September 21, 2025
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

September 21, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

September 21, 2025
GGI

Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji  Sheik Shamsudeen

September 21, 2025
Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori

Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.