• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

bySani Anwar
2 years ago
Gishiri

Masana harkokin kiwon lafiya, sun gargadi ‘yan Nijeriya kan yin amfani da wasu kayayyakin masarufi, wadanda a hukumance ba a bayar da izinin yin amfani da su ba, ciki har da wani sinadari gishiri, wanda a yanzu haka yana iya cutar da lafiyar Dan Adam, sakamakon illar da ke tattare da shi kamar yadda Royal Ibeh ya bayyana.

Har ila yau, masana harkokin kiwon lafiyar da kwararru a kan harkar sarrafa abinci, sun yi wannan gargadi tare da jan hankulan ‘yan Nijeriya, da su zama masu lura a kan ire-iren abincin da za su kai kofar bakunansu.

  • Dan Majalisa Zai Aurar Da Mata Marayu 100 A Kebbi
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

A ‘yan kwanakin nan ne, aka samu a wasu yankunan Arewacin Nijeriya, an kai wani sinadarin gishiri; wanda a hukumance babu izinin yin amfani da ana sayarwa, inda ba tare da wani bata lokaci ba; masana suka bayar da sanarwar cewa, ba mai inganci ba ne; zai kuma iya cutarwa.

“Wannan wani sinadarin gishiri ne, mai karfin gaske da aka jima ana amfani da shi shekara da shekaru, don kara dandano da kawata girkin abinci.

Wani kwararre a kan harkar sarrafa abinci, Isah Kareem ya bayyana cewa, wajibi ne mutane su lura da irin sinadaren kayan abincin da suke amfani da su a gargajiyance, don kara dandanon abincinsu na yau da kullum, domin kauce wa fada wa hadarin cutar da lafiyarsu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Ya kara da cewa, “duk dadin da abinci zai yi idan aka yi amfani da ire-iren wadannan abubuwan da hukuma ba ta bayar da izinin yin amfani da su ba, a bar su ya fi alhairi domin kuwa ko shakka babu akwai hadari a tattare da su.

Sannan, ire-iren wannan gishiri, ana sayar da shi a bude ba kamar irin sauran kayan kamfani da ake adana su da kyau ba, duk da dai masu saye na rububunsa ne; saboda ganin garabasa ko arha, wanda kuma ita arha kamar yadda masu iya magana ke fada, ba ta ado.

Haka zalika, sinadarin gishirin da Hukumar NAFDAC ta amince a yi amfani da su sun hada da; Ajinomoto, Beda da sauran makamantansu, wadanda suke a cikin sacet na leda a killace ake sayar da su. Amma wadannan; wadanda ba a cikin sacet na leda suke ba, kai tsaye sun sha ban-ban da wancan.

Don haka, babu ta yadda za a iya gane alama ko wata sheda ta kamfani, ballantana a iya tabbatar da ingancinsa. Kari a kan hakan shi ne, ana sayar da shi da matukar arha; wanda duk mai hankali zai iya tabbatar da cewa, lallai wannan ba abu ne mai inganci ba, sannan kai tsaye zai iya cutarwa”.

Wata masaniya harkokin kiwon lafiyar, Foloke Ojo ta bayyana yadda a kullum ta duniya, ake kai ire-iren wadannan kayan amfanin abinci ake sayarwa, shi kuma mai saye babu abin da ke gabansa, illa dandanon da zai samu da kuma arhar abin sayarwar. Sannan, wasu ma amfani suke yi da sunayen wasu kamfanonin tare da ikirarin cewa, hajar tasu ta fi kowace haja kyau da inganci.

Ta kara da cewa, “kai ire-iren wadannan kaya tare da sayar da su a kasuwanni, ya jima da zama ruwan dare. Duk da cewa, Hukumar NAFDAC da ta SON, na bibiyar kasuwannin suna bincikawa, don bankado kayan jabu da wadanda hukuma ba ta bayar da izinin sayar da su ba”, in ji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa - Buhari

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version