• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya

by Sani Anwar
2 years ago
in Labarai
0
Masana Sun Yi Gargadi Kan Amfani Da Wani Sinadarin Gishiri A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin kiwon lafiya, sun gargadi ‘yan Nijeriya kan yin amfani da wasu kayayyakin masarufi, wadanda a hukumance ba a bayar da izinin yin amfani da su ba, ciki har da wani sinadari gishiri, wanda a yanzu haka yana iya cutar da lafiyar Dan Adam, sakamakon illar da ke tattare da shi kamar yadda Royal Ibeh ya bayyana.

Har ila yau, masana harkokin kiwon lafiyar da kwararru a kan harkar sarrafa abinci, sun yi wannan gargadi tare da jan hankulan ‘yan Nijeriya, da su zama masu lura a kan ire-iren abincin da za su kai kofar bakunansu.

  • Dan Majalisa Zai Aurar Da Mata Marayu 100 A Kebbi
  • Zaben Kano: ‘Yansanda Da Masu Zanga-zanga Sun Yi Arangama A Kano

A ‘yan kwanakin nan ne, aka samu a wasu yankunan Arewacin Nijeriya, an kai wani sinadarin gishiri; wanda a hukumance babu izinin yin amfani da ana sayarwa, inda ba tare da wani bata lokaci ba; masana suka bayar da sanarwar cewa, ba mai inganci ba ne; zai kuma iya cutarwa.

“Wannan wani sinadarin gishiri ne, mai karfin gaske da aka jima ana amfani da shi shekara da shekaru, don kara dandano da kawata girkin abinci.

Wani kwararre a kan harkar sarrafa abinci, Isah Kareem ya bayyana cewa, wajibi ne mutane su lura da irin sinadaren kayan abincin da suke amfani da su a gargajiyance, don kara dandanon abincinsu na yau da kullum, domin kauce wa fada wa hadarin cutar da lafiyarsu.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Ya kara da cewa, “duk dadin da abinci zai yi idan aka yi amfani da ire-iren wadannan abubuwan da hukuma ba ta bayar da izinin yin amfani da su ba, a bar su ya fi alhairi domin kuwa ko shakka babu akwai hadari a tattare da su.

Sannan, ire-iren wannan gishiri, ana sayar da shi a bude ba kamar irin sauran kayan kamfani da ake adana su da kyau ba, duk da dai masu saye na rububunsa ne; saboda ganin garabasa ko arha, wanda kuma ita arha kamar yadda masu iya magana ke fada, ba ta ado.

Haka zalika, sinadarin gishirin da Hukumar NAFDAC ta amince a yi amfani da su sun hada da; Ajinomoto, Beda da sauran makamantansu, wadanda suke a cikin sacet na leda a killace ake sayar da su. Amma wadannan; wadanda ba a cikin sacet na leda suke ba, kai tsaye sun sha ban-ban da wancan.

Don haka, babu ta yadda za a iya gane alama ko wata sheda ta kamfani, ballantana a iya tabbatar da ingancinsa. Kari a kan hakan shi ne, ana sayar da shi da matukar arha; wanda duk mai hankali zai iya tabbatar da cewa, lallai wannan ba abu ne mai inganci ba, sannan kai tsaye zai iya cutarwa”.

Wata masaniya harkokin kiwon lafiyar, Foloke Ojo ta bayyana yadda a kullum ta duniya, ake kai ire-iren wadannan kayan amfanin abinci ake sayarwa, shi kuma mai saye babu abin da ke gabansa, illa dandanon da zai samu da kuma arhar abin sayarwar. Sannan, wasu ma amfani suke yi da sunayen wasu kamfanonin tare da ikirarin cewa, hajar tasu ta fi kowace haja kyau da inganci.

Ta kara da cewa, “kai ire-iren wadannan kaya tare da sayar da su a kasuwanni, ya jima da zama ruwan dare. Duk da cewa, Hukumar NAFDAC da ta SON, na bibiyar kasuwannin suna bincikawa, don bankado kayan jabu da wadanda hukuma ba ta bayar da izinin sayar da su ba”, in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus

Next Post

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa – Buhari

Related

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

6 minutes ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

1 hour ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

10 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

12 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

12 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

14 hours ago
Next Post
Matsayin Da Dimukradiyyar Nijeriya Ta Kai A Yanzu – Buhari

Ba Na Kewar Fadar Shugaban Kasa - Buhari

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.