• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana’antun Nijeriya Sun Kashe Naira Tiriliyan 1.11 Wajen Samun Wutar Lantarki A 2024 – Rahoto

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
TCN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sashin masana’antu a Nijeriya na fuskantar matsalolin ciki har da ma na tattalin arziki, inda masu gudanar da sashin suka kashe adadin naira Tiriliyan 1.11 wajen neman hanyoyinsamar da wutan lantarki a shekarar 2024, tare da sallamar adadin ma’aikata 17,949.

 

A cewar rahoton da kungiyar masana’antu a Nijeriya (MAN) ta fitar, ya nuna cewa an samu karin kaso 42.3 daga naira biliyan 781.68 da aka kashe kan wannan manufar a shekarar 2023.

  • An Sako Malamin Kiristan Cocin Katolika Da Aka Sace A Kaduna
  • Idan Kana Son Barin PDP, Yanzu Ne Lokacin – Bukola Saraki

Rahoton ya ce bangaren samar da abinci da abin sha sun kashe naira biliyan 229.41 a bangaren makamashi, sama da naira biliyan 182.76 a shekarar 2023, yayin da kudin makamashin sinadarai da magunguna ya rubanya zuwa naira biliyan 208.68.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Sashin ma’adinai da ba na karfe ba ta kashe kudin makamashi da kashi 33.7 zuwa naira biliyan 118.49, kuma masana’antar yadi, tufafi da takalmi kudin da ya kashe ya karu sau hudu, wanda ya kai naira biliyan 26.45 a shekarar 2024, idan aka kwatanta da naira biliyan 6.97 a shekarar 2023.

 

Rahoton ya ce duk da an samu karin wutar lantarki a cikin masana’antu a shekarar 2024, da adadin karin wuta na awa 13.3 a kwace ranar da ya karu daga awa 10.6 a shekarar 2023.

 

Kazalika karin kudin wuta ya karu da kaso 200 ga wadanda suke amfani da rukunin A, don haka kudaden da masana’antun ke kashewa wajen biyan kudin wuta nan ma ya karu sosai.

 

“A daidai lokacin da aka samu karin wutar lantarki, masana’antu da dama har yanzu suna fuskantar daukewar wuta a kai a kai, da tsadar wutan duk da kasar kuma ta fuskanci lalacewar babban layin wuta har sau 12, wanann shi ne babban abun damuwa.

 

“A neman mafita ga yawan daukewar wutar da karin farashin kudin mai da gas duk sun mamaye masana’antu,” rahoton ya shaida.

 

A daidai wannan gabar, adadin mutanen da suke barin aiki a kamfanoni ya karu daga 17,364 a 2023 zuwa 17,949 a shekarar 2024. A gefe guda kuma an samu sabbin ma’aikata 16,820 a 2024.

 

Dangane da saka hannun jari a fannin da ake samu, an ce fannin ya samu raguwar zuba jarin masana’antu da kashi 35.3 a duk shekara zuwa naira biliyan 658.81 a shekarar 2024, lamarin da ke nuni da rashin tabbas na tattalin arziki da kuma rage tsare-tsaren fadada ayyukan.

 

Rahoton ya kara da cewa, jimillar jarin ya ragu da kashi 11.3 zuwa naira tiriliyan 2.85, inda a bangaren filayen da gine-gine da kayan daki da sauran kayayyaki suka samu koma-baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Taron Dandalin Tattaunawar Afirka Ta Yamma Karo Na Farko A Senegal

Next Post

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

Related

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

14 minutes ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

1 hour ago
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn
Labarai

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

4 hours ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

11 hours ago
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu
Labarai

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

12 hours ago
Next Post
Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam'iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka - Bukola Saraki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.