Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Asabar cewa, a bisa gayyatar memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin kuma daraktan ofishin hukumar kula da harkokin waje na kwamitin koli, Wang Yi, mai baiwa shugaban kasar Amurka shawara kan harkokin tsaro Jake Sullivan, zai ziyarci kasar Sin daga ranar a 27 zuwa ta 29 ga Agusta. Kuma bangarorin biyu za su gudanar da wani sabon zagaye na muhimmin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka. (Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp