ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

by Sani Anwar and Sulaiman
2 years ago
Kayan marmari

Wani kwararren likita a Nijeriya, Dakta Ben Ahunonu; ya gargadi ‘yan Nijeriya kan amfani da kayan marmarin da aka jima da yankawa da ake sayarwa a kan hanya.

 

Likitan ya kara da cewa, wadannan kayan marmari da suka hada da Abarba, Gwanda, Kankana da sauran makamantansu; ana yankawa ana sayarwa a kan titina da sauran hanyoyi, wadanda kuma sanin kowa ne kwari kamar irin su Kuda na bin su; a duk ire-iren wadannan gurare da ake gudanar da wannan sana’a.

ADVERTISEMENT
  • Baturiya Mafi Tsufa A Duniya Ta Rasu
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

“Yanka ire-iren wadannan kayan marmari ana sayarwa, na tattare da matsaloli da dama; musamman ganin cewa ana yanka kayan itatuwan su jima kafin a yi amfani da su, wasu tun safe ake yankawa; haka za su kai har dare, wasu ma su kwana su kara kwana; sannan a haka za a sayarwa da mutane.”

 

LABARAI MASU NASABA

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Saboda haka a cewar tasa, akwai wasu kwayoyin cuta da ke tattare da irin wadannan kayan marmari; sakamakon barin su da ake yi su jima a ajiye bayan an yanka su.

 

“Kudajen da ke bin wadannan kayan marmari, na iya kasancewa ko dauke da wasu kwayoyin cuta; wadanda ka iya haifar da wasu cututtuka kamar; gudawa, ciwon zazzabi (typhoid) da kuma cutar kwalara”, a cewar Daktan.

 

Don haka, sai ya ba da shawarar cewa; cin dukkanin ‘ya’yan itatuwa ko kayan marmari, abu ne da ya kyautu a kula da shi tare da yin nazari sosai; musamman ta fuskar sanya kudi wajen saya da kuma yin la’akari da amfaninsa a jiki.

 

“Saboda galibi bayan an yanka su; iska ta gama ratsa jikinsu, babu wuya suke fara daukar hanyar lalacewa.

 

“Mafi yawan mutane, ba su da ilimin cewa; bawon jikin ‘ya’yan itatuwa su ne ke kare dukkanin abin da ke cikinsu, da zarar an yanka; babu kuma abin da zai kare abin da ke ciki. Shi yasa ake ba da shawarar cewa, ka da a yanka sai an tashi amfani da shi”, in ji shi.

 

Saboda haka, ya sake shawartar mutane da cewa; duk yayin da suka tashi sayen kayan marmari, wajibi ne su duba tare da tabbatar da cewa; bai lalace ba. Dalili kuwa, dukkan kayan marmari masu kyau; wadanda kuma aka yanka nan take, su ne ke da amfani tare da gina jiki.

 

Har ila yau a cewar likitan, kayan itatuwar da aka riga aka yanka; amfaninsu na raguwa idan ba a yi amfani da su nan take ba. Ma’ana, idan aka yanka aka bari suka dauki wani tsawon wani lokaci ba a ci ko an sha ba, amfaninsu na samun koma baya; idan aka kwatanta da wanda aka yanka, aka yi amfani da shi nan take.

 

Haka nan, idan aka ji ya fara canzawa ta fuskar dandano ko warinsa; a nan ya zama wajibi a zubar da shi, ka da a yarda a ci ko a sha.

 

A karshe, ya yi nuni da cewa; idan so samu ne, gwara mutum ya sayi kwallon kayan itatuwar da yake bukata; amma sakamakon matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu, mutum zai iya tsayawa ya kula sosai da yanayin wurin da zai sayi wanda aka yanka din tare kuma da duba nagartar wanda zai saya.

Kayan marmari
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Kayan marmari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Sulaiman
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kiwon Lafiya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.