ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

by Sani Anwar and Sulaiman
2 years ago
Kayan marmari

Wani kwararren likita a Nijeriya, Dakta Ben Ahunonu; ya gargadi ‘yan Nijeriya kan amfani da kayan marmarin da aka jima da yankawa da ake sayarwa a kan hanya.

 

Likitan ya kara da cewa, wadannan kayan marmari da suka hada da Abarba, Gwanda, Kankana da sauran makamantansu; ana yankawa ana sayarwa a kan titina da sauran hanyoyi, wadanda kuma sanin kowa ne kwari kamar irin su Kuda na bin su; a duk ire-iren wadannan gurare da ake gudanar da wannan sana’a.

ADVERTISEMENT
  • Baturiya Mafi Tsufa A Duniya Ta Rasu
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

“Yanka ire-iren wadannan kayan marmari ana sayarwa, na tattare da matsaloli da dama; musamman ganin cewa ana yanka kayan itatuwan su jima kafin a yi amfani da su, wasu tun safe ake yankawa; haka za su kai har dare, wasu ma su kwana su kara kwana; sannan a haka za a sayarwa da mutane.”

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

Saboda haka a cewar tasa, akwai wasu kwayoyin cuta da ke tattare da irin wadannan kayan marmari; sakamakon barin su da ake yi su jima a ajiye bayan an yanka su.

 

“Kudajen da ke bin wadannan kayan marmari, na iya kasancewa ko dauke da wasu kwayoyin cuta; wadanda ka iya haifar da wasu cututtuka kamar; gudawa, ciwon zazzabi (typhoid) da kuma cutar kwalara”, a cewar Daktan.

 

Don haka, sai ya ba da shawarar cewa; cin dukkanin ‘ya’yan itatuwa ko kayan marmari, abu ne da ya kyautu a kula da shi tare da yin nazari sosai; musamman ta fuskar sanya kudi wajen saya da kuma yin la’akari da amfaninsa a jiki.

 

“Saboda galibi bayan an yanka su; iska ta gama ratsa jikinsu, babu wuya suke fara daukar hanyar lalacewa.

 

“Mafi yawan mutane, ba su da ilimin cewa; bawon jikin ‘ya’yan itatuwa su ne ke kare dukkanin abin da ke cikinsu, da zarar an yanka; babu kuma abin da zai kare abin da ke ciki. Shi yasa ake ba da shawarar cewa, ka da a yanka sai an tashi amfani da shi”, in ji shi.

 

Saboda haka, ya sake shawartar mutane da cewa; duk yayin da suka tashi sayen kayan marmari, wajibi ne su duba tare da tabbatar da cewa; bai lalace ba. Dalili kuwa, dukkan kayan marmari masu kyau; wadanda kuma aka yanka nan take, su ne ke da amfani tare da gina jiki.

 

Har ila yau a cewar likitan, kayan itatuwar da aka riga aka yanka; amfaninsu na raguwa idan ba a yi amfani da su nan take ba. Ma’ana, idan aka yanka aka bari suka dauki wani tsawon wani lokaci ba a ci ko an sha ba, amfaninsu na samun koma baya; idan aka kwatanta da wanda aka yanka, aka yi amfani da shi nan take.

 

Haka nan, idan aka ji ya fara canzawa ta fuskar dandano ko warinsa; a nan ya zama wajibi a zubar da shi, ka da a yarda a ci ko a sha.

 

A karshe, ya yi nuni da cewa; idan so samu ne, gwara mutum ya sayi kwallon kayan itatuwar da yake bukata; amma sakamakon matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu, mutum zai iya tsayawa ya kula sosai da yanayin wurin da zai sayi wanda aka yanka din tare kuma da duba nagartar wanda zai saya.

Kayan marmari
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
Kayan marmari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.