ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

by Sani Anwar and Sulaiman
2 years ago
Kayan marmari

Wani kwararren likita a Nijeriya, Dakta Ben Ahunonu; ya gargadi ‘yan Nijeriya kan amfani da kayan marmarin da aka jima da yankawa da ake sayarwa a kan hanya.

 

Likitan ya kara da cewa, wadannan kayan marmari da suka hada da Abarba, Gwanda, Kankana da sauran makamantansu; ana yankawa ana sayarwa a kan titina da sauran hanyoyi, wadanda kuma sanin kowa ne kwari kamar irin su Kuda na bin su; a duk ire-iren wadannan gurare da ake gudanar da wannan sana’a.

ADVERTISEMENT
  • Baturiya Mafi Tsufa A Duniya Ta Rasu
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

“Yanka ire-iren wadannan kayan marmari ana sayarwa, na tattare da matsaloli da dama; musamman ganin cewa ana yanka kayan itatuwan su jima kafin a yi amfani da su, wasu tun safe ake yankawa; haka za su kai har dare, wasu ma su kwana su kara kwana; sannan a haka za a sayarwa da mutane.”

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

Saboda haka a cewar tasa, akwai wasu kwayoyin cuta da ke tattare da irin wadannan kayan marmari; sakamakon barin su da ake yi su jima a ajiye bayan an yanka su.

 

“Kudajen da ke bin wadannan kayan marmari, na iya kasancewa ko dauke da wasu kwayoyin cuta; wadanda ka iya haifar da wasu cututtuka kamar; gudawa, ciwon zazzabi (typhoid) da kuma cutar kwalara”, a cewar Daktan.

 

Don haka, sai ya ba da shawarar cewa; cin dukkanin ‘ya’yan itatuwa ko kayan marmari, abu ne da ya kyautu a kula da shi tare da yin nazari sosai; musamman ta fuskar sanya kudi wajen saya da kuma yin la’akari da amfaninsa a jiki.

 

“Saboda galibi bayan an yanka su; iska ta gama ratsa jikinsu, babu wuya suke fara daukar hanyar lalacewa.

 

“Mafi yawan mutane, ba su da ilimin cewa; bawon jikin ‘ya’yan itatuwa su ne ke kare dukkanin abin da ke cikinsu, da zarar an yanka; babu kuma abin da zai kare abin da ke ciki. Shi yasa ake ba da shawarar cewa, ka da a yanka sai an tashi amfani da shi”, in ji shi.

 

Saboda haka, ya sake shawartar mutane da cewa; duk yayin da suka tashi sayen kayan marmari, wajibi ne su duba tare da tabbatar da cewa; bai lalace ba. Dalili kuwa, dukkan kayan marmari masu kyau; wadanda kuma aka yanka nan take, su ne ke da amfani tare da gina jiki.

 

Har ila yau a cewar likitan, kayan itatuwar da aka riga aka yanka; amfaninsu na raguwa idan ba a yi amfani da su nan take ba. Ma’ana, idan aka yanka aka bari suka dauki wani tsawon wani lokaci ba a ci ko an sha ba, amfaninsu na samun koma baya; idan aka kwatanta da wanda aka yanka, aka yi amfani da shi nan take.

 

Haka nan, idan aka ji ya fara canzawa ta fuskar dandano ko warinsa; a nan ya zama wajibi a zubar da shi, ka da a yarda a ci ko a sha.

 

A karshe, ya yi nuni da cewa; idan so samu ne, gwara mutum ya sayi kwallon kayan itatuwar da yake bukata; amma sakamakon matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu, mutum zai iya tsayawa ya kula sosai da yanayin wurin da zai sayi wanda aka yanka din tare kuma da duba nagartar wanda zai saya.

Kayan marmari
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Kayan marmari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
Manyan Labarai

Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”

September 3, 2026
Kayan marmari
Kiwon Lafiya

2 – 3 Cikin 10 Na Masu Cutar Diphtheria Na Iya Mutuwa A Katsina – NMA

August 30, 2026
Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
Kiwon Lafiya

Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?

August 29, 2026
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.