• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Bayyana Ra’ayi Sun Amince Ruhin SCO Ne Sabon Salon Raya Huldar Kasa Da Kasa

by Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Masu Bayyana Ra’ayi Sun Amince Ruhin SCO Ne Sabon Salon Raya Huldar Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka hankulan duniya sun karkata ga kungiyar hadin gwiwar Shanghai ko SCO, wadda a matsayinta na kungiyar hadin gwiwa ta kasashe mafiya girma da yawan al’umma a duniya, shugabannin kasashe mambobinta suka hallara a kasar Kazakhstan, domin tattauna batutuwan da suka shafi tsaro da ci gaban shiyyarsu.

Wani sakamakon kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta fitar ya nuna cewa, masu bayyana ra’ayi na da imanin cewa, bayan shekaru sama da 20 na samun ci gaba, kungiyar SCO ta zamo garkuwar tsaro, kuma gadar hadin gwiwa, kana kafar yaukaka abota, kana wani babban karfi na gina shiyyar.

  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron AI Na 2024
  • Sin Na Fatan Za A Inganta Ci Gaban Fasahar AI Cikin Lumana

Kaso 82.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na fatan kungiyar SCO za ta zamo kakaki ga kasashe masu tasowa, kana za ta yayata kafuwar tsarin gudanar da harkokin duniya bisa daidaito da sanin ya kamata.

Kasancewar tsaro tushen ci gaba, a matsayinta na mambar kungiyar ta SCO, shawarar wanzar da tsaro a duniya da kasar Sin ta gabatar ta yi daidai da manufar tabbatar da tsaro ta SCO, wanda masu bayyana ra’ayin daga sassan duniya daban daban suka tabbatar da hakan. Cikin masu bayyana hakan, kaso 91.2 bisa dari sun amince cewa, ana iya warware bambance-bambance, da rashin jituwa tsakanin kasashe ne kadai ta hanyar tattaunawa da gudanar da shawarwari, maimakon kakaba takunkumai da yankewa wasu sassa hukunci na radin kai.

Kaza lika, kaso 94.8 bisa dari sun amince tunanin yakin cacar baka, ba abun da zai haifar sai koma-baya ga manufar wanzar da zaman lafiya ta duniya, da danniya, da siyasar nuna karfin tuwo, matakan da kuma za su jefa zaman lafiyar duniya cikin hadari, yayin da fito-na-fito tsakanin kananan rukunoni zai dada fadada kalubalolin tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Kafar CGTN ta kasar Sin ce ta fitar da sakamakon kuri’un na jin ra’ayin jama’a ta harsunan Turanci, da Faransanci, da Larabci, da harsunan Sifaniya da Rasha, bayan kada kuri’un mutane 13,527 cikin sa’o’i 24.  (Saminu Alhassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Duniya Ya Bai Wa Nijar Tallafin Biliyan 214

Next Post

An Watsa Shirin “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” Ta Kafofin Yada Labaran Kazakhstan

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

5 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

7 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

8 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

9 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
An Watsa Shirin “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” Ta Kafofin Yada Labaran Kazakhstan

An Watsa Shirin “Bayanan Magabata Da Xi Jinping Yake So” Ta Kafofin Yada Labaran Kazakhstan

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.