• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu garkuwa Sun Rage Farashin Kuɗin Fansar Matar Sarki Bayan Sun Kashe Sarkin A Kwara

by Muhammad
2 years ago
in Al'ajabi, Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Masu garkuwa Sun Rage Farashin Kuɗin Fansar Matar Sarki Bayan Sun Kashe Sarkin A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindigar da suka kashe wani Sarki a jihar Kwara tare da yin garkuwa da matarsa ​​da wani mutum guda sun rage kudin fansar da suka fada tun da farko daga miliyan N100 zuwa Naira miliyan 40.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa a ranar Lahadi ‘yan bindigar suka fara tuntubar iyalan Sarkin kan biyan Naira miliyan 100 na kudin fansa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sarki Da Yin Awon Gaba Da Matarsa Da Wasu Mutum 2 A Kwara
  • Jami’an Tsaro Sun Kama Ɗan Bindigar Da Ake Zargi Da Kashe Nabeeha

An kashe Sarkin, Oba Olusegun Aremu-Cole, wanda shi ne Olukoro na Koro-Ekiti a karamar hukumar Ekiti (LGA) ta jihar Kwara, a fadarsa a daren ranar Alhamis.

A lokaci guda maharan sun yi awon gaba da matarsa ​​da wani mutum guda.

Da yake magana da manema labarai a yammacin ranar Lahadi, Kehinde Bayode, shugaban kwamitin aiwatar da mulki (TIC) a karamar hukumar Ekiti ta jihar Kwara, ya ce an kama wani da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Ya ce an kama wanda ake zargin ne a garin Eruku da ke karamar hukumar Ekiti ranar Lahadi.

Yayin da yake magana kan kokarin da aka yi na kubutar da matar sarkin da aka yi garkuwa da ita da kuma wani mutum, Bayode ya ce: “Masu garkuwa da mutanen sun tuntubi iyalan.

“Suna neman kudin fansa Naira miliyan 100, wanda a yanzu an mayar da shi Naira miliyan 40.

“Amma har yanzu muna tattaunawa da su kuma a yanzu haka, ina kan hanyar zuwa Koro don samun sabbin bayanai kan tattaunawar.

“Za mu ci gaba da yi muku bayani (‘yan jarida) kan yadda lamarin ke wakana,” Cewarsa a yammacin ranar Lahadi.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, bai tabbatar da kama ko mutum guda ko wani da ake zargi ba.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya tura wata tawagar zuwa Koro-Ekiti domin lalubo wadanda suka aikata laifin.

“’Yan sanda suna aiki tare da sauran jami’an tsaro domin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su.

“Ba a kama shi ba tukuna. Za mu sanar da ku abubuwan da ke wakana yayin da zarar an samu nasarar kama masu laifin,” cewar ‘yansanda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudin FansaKwaraMasu GarkuwaMatar Sarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

DA ƊUMI-ƊUMI: Mata Na Gudanar Da Zanga-zanga Kan Tsananin Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Neja

Next Post

ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

Related

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

1 hour ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

2 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

14 hours ago
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

16 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

19 hours ago
Next Post
ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.