• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu garkuwa Sun Rage Farashin Kuɗin Fansar Matar Sarki Bayan Sun Kashe Sarkin A Kwara

by Muhammad
2 years ago
in Al'ajabi, Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Masu garkuwa Sun Rage Farashin Kuɗin Fansar Matar Sarki Bayan Sun Kashe Sarkin A Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindigar da suka kashe wani Sarki a jihar Kwara tare da yin garkuwa da matarsa ​​da wani mutum guda sun rage kudin fansar da suka fada tun da farko daga miliyan N100 zuwa Naira miliyan 40.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa a ranar Lahadi ‘yan bindigar suka fara tuntubar iyalan Sarkin kan biyan Naira miliyan 100 na kudin fansa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sarki Da Yin Awon Gaba Da Matarsa Da Wasu Mutum 2 A Kwara
  • Jami’an Tsaro Sun Kama Ɗan Bindigar Da Ake Zargi Da Kashe Nabeeha

An kashe Sarkin, Oba Olusegun Aremu-Cole, wanda shi ne Olukoro na Koro-Ekiti a karamar hukumar Ekiti (LGA) ta jihar Kwara, a fadarsa a daren ranar Alhamis.

A lokaci guda maharan sun yi awon gaba da matarsa ​​da wani mutum guda.

Da yake magana da manema labarai a yammacin ranar Lahadi, Kehinde Bayode, shugaban kwamitin aiwatar da mulki (TIC) a karamar hukumar Ekiti ta jihar Kwara, ya ce an kama wani da ake zargi.

Labarai Masu Nasaba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

Ya ce an kama wanda ake zargin ne a garin Eruku da ke karamar hukumar Ekiti ranar Lahadi.

Yayin da yake magana kan kokarin da aka yi na kubutar da matar sarkin da aka yi garkuwa da ita da kuma wani mutum, Bayode ya ce: “Masu garkuwa da mutanen sun tuntubi iyalan.

“Suna neman kudin fansa Naira miliyan 100, wanda a yanzu an mayar da shi Naira miliyan 40.

“Amma har yanzu muna tattaunawa da su kuma a yanzu haka, ina kan hanyar zuwa Koro don samun sabbin bayanai kan tattaunawar.

“Za mu ci gaba da yi muku bayani (‘yan jarida) kan yadda lamarin ke wakana,” Cewarsa a yammacin ranar Lahadi.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, bai tabbatar da kama ko mutum guda ko wani da ake zargi ba.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya tura wata tawagar zuwa Koro-Ekiti domin lalubo wadanda suka aikata laifin.

“’Yan sanda suna aiki tare da sauran jami’an tsaro domin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su.

“Ba a kama shi ba tukuna. Za mu sanar da ku abubuwan da ke wakana yayin da zarar an samu nasarar kama masu laifin,” cewar ‘yansanda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudin FansaKwaraMasu GarkuwaMatar Sarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

DA ƊUMI-ƊUMI: Mata Na Gudanar Da Zanga-zanga Kan Tsananin Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Neja

Next Post

ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

4 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

6 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

7 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

19 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

21 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

24 hours ago
Next Post
ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.