ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu garkuwa Sun Rage Farashin Kuɗin Fansar Matar Sarki Bayan Sun Kashe Sarkin A Kwara

by Muhammad
2 years ago
Kwara

‘Yan bindigar da suka kashe wani Sarki a jihar Kwara tare da yin garkuwa da matarsa ​​da wani mutum guda sun rage kudin fansar da suka fada tun da farko daga miliyan N100 zuwa Naira miliyan 40.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa a ranar Lahadi ‘yan bindigar suka fara tuntubar iyalan Sarkin kan biyan Naira miliyan 100 na kudin fansa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sarki Da Yin Awon Gaba Da Matarsa Da Wasu Mutum 2 A Kwara
  • Jami’an Tsaro Sun Kama Ɗan Bindigar Da Ake Zargi Da Kashe Nabeeha

An kashe Sarkin, Oba Olusegun Aremu-Cole, wanda shi ne Olukoro na Koro-Ekiti a karamar hukumar Ekiti (LGA) ta jihar Kwara, a fadarsa a daren ranar Alhamis.

ADVERTISEMENT

A lokaci guda maharan sun yi awon gaba da matarsa ​​da wani mutum guda.

Da yake magana da manema labarai a yammacin ranar Lahadi, Kehinde Bayode, shugaban kwamitin aiwatar da mulki (TIC) a karamar hukumar Ekiti ta jihar Kwara, ya ce an kama wani da ake zargi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya ce an kama wanda ake zargin ne a garin Eruku da ke karamar hukumar Ekiti ranar Lahadi.

Yayin da yake magana kan kokarin da aka yi na kubutar da matar sarkin da aka yi garkuwa da ita da kuma wani mutum, Bayode ya ce: “Masu garkuwa da mutanen sun tuntubi iyalan.

“Suna neman kudin fansa Naira miliyan 100, wanda a yanzu an mayar da shi Naira miliyan 40.

“Amma har yanzu muna tattaunawa da su kuma a yanzu haka, ina kan hanyar zuwa Koro don samun sabbin bayanai kan tattaunawar.

“Za mu ci gaba da yi muku bayani (‘yan jarida) kan yadda lamarin ke wakana,” Cewarsa a yammacin ranar Lahadi.

Sai dai jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, bai tabbatar da kama ko mutum guda ko wani da ake zargi ba.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya tura wata tawagar zuwa Koro-Ekiti domin lalubo wadanda suka aikata laifin.

“’Yan sanda suna aiki tare da sauran jami’an tsaro domin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su.

“Ba a kama shi ba tukuna. Za mu sanar da ku abubuwan da ke wakana yayin da zarar an samu nasarar kama masu laifin,” cewar ‘yansanda.

Kwara
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

ADP Ta Doke NNPP, Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Cike-gurbi Na Mazaɓar Sanatan Filato Ta Arewa

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.