• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar dillalan masu sana’ar Bola-jari ta Nijeriya ta kasa, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta ba su lamuni mai sauki domin fadada harkokin kasuwancinsu.

Dillalan na jari-bola sun kuma bukaci gwamnati da ta yi duba kan hukumomin tsaro da su daina muzgunawa mambobinsu.

  • Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja
  • Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

Shugaban shugabannin kungiyar, Alhaji Aminu Hassan, ne ya yi wannan roko a taron masu ruwa da tsaki na kungiyar a ranar Lahadi a Abuja.

Kungiyar ta masu sana’ar Bola-jari, kungiya ce da take da rijista a hukumance a karkashin dokar kungiyar kwadago, Cap. T14, na dokokin Tarayyar Nijeriya 2004.

Ita ce jigo ta duk mutanen da ke sana’ar Bola-jari, kuma take rarrabawa kamfanoni masu sarrafa lallatattun kaya su juya su zuwa sababbi kaya.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Masana sun ce sana’ar tana samun sama da Naira tiriliyan daya a duk shekara.

A cewar Hassan, kungiyar na matukar bukatar kudade da kariya domin bunkasa gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin kasa.

“Muna da mambobi har miliyan biyar, amma suna aiki a cikin yanayi mai wahala,” in ji shi.

Hassan ya yi zargin cewa jami’an tsaro na cin zarafinsu “musamman wajen isar da kayayyakinmu ga kamfanonin da ke hakar man fetur”.

“Saboda haka, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani ta kuma taimaka mana wajen bin diddigin wannan mugunyar dabi’ar domin ba mu damar gudanar da harkokinmu ba tare da wata matsala ba.

“A jihar Kano kadai muna da mambobi kusan miliyan guda da suke bazuwa a fadin jihar ba a maganar jihar Legas inda muke da mambobi kusan miliyan biyu a sana’ar Bola-jari.

Shugaban ya kara da cewa “Kasuwancin da ke da dimbin mambobi sun cancanci tallafin kudi da kariya daga gwamnatin tarayya don ba su damar yin aiki yadda ya kamata.”

Hassan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sa baki kan farashin kayayyakin da suke sayar da su, kar a bar wa kamfanonin da suke kasuwanci da su.

“Wadannan kamfanoni, galibin kamfanonin kasashen waje, mallakar Sinawa da Indiyawa, suna sha’awar canza farashin kayayyakin da suke saya daga gare mu yadda suke so, wani lokacin ba tare da sanar da mu, masu kawo kayayyaki ba.

“Wannan ci gaban ya shafi kasuwancinmu sosai.

“Misali, za ku iya siyan kaya a kan Naira 500,000, amma idan kun isa kamfanin, za su ce muku ba za su iya siyan sa fiye da N400,000 ba.

“Wannan yakan haifar da babban rashi ko asara daga bangarenmu. Ka yi tunani bayan ka sayi samfur akan N500,000 kawai ka gama sai ka siyar da shi akan N400,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bola-jariGwamnatin NijeriyaNijeriyaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidauniyar Agaji Ta Qatar Za Ta Gina Gidaje 500,000 Ga Marasa Ƙarfi A Kaduna –Uba Sani

Next Post

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

15 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

16 hours ago
Next Post
Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.