• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Son Shiga Harkar Fim Su Riki Biyayya Da Kyau – Abba Harara

by Rabi'at Sidi Bala
3 years ago
Harara

A Karshen tattaunawar da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA ta yi da shahararren marubucin fim kuma mai shiryawa a cikin masana’antar Kannywood, wanda ya shafe shekaru goma yana rubuta fim wato Abba Harara, ya bayyana wa masu karatu ra’ayinsa dangane da fitowa matsayin jarumi, ya kuma yi karin haske game da yadda ya dauki fim a wajensa, tare da irin kalubale da nasarorin da ya samu, har ma da wasu batutuwan da suka shafi sana’arsa ta fim. Sannan ya ja hankalin masu sha’awar shiga harkar fim da su yi biyayya ga na gaba domin samun nasara. Ga dai tattaunawar kamar haka:

Kamar da wanne lokaci ka fi jin dadin yin rubutu?
Na fi jin dadin yin rubutu kamar da Asuba da kuma tsakiyar dare.

Wanne fim ne ya zama bakandamiyarka wanda ka rubuta da wanda ka shirya?
RUHIN MIJINA ne Bakandamiyata a fina-finai da na rubuta. A wanda na shirya kuma ‘MALAMIN KAUNA’ ne Bakandamiyata.

Harara

Ko akwai wani kalubale da ka taba fuskanta game da harkar rubutu ko kuma shirya fim?
Akwai kalubale da na fuskanta tabbas a game da rubutu da kuma shirya fim.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Kamar wadanne irin kalubale kenan?
Kalubalen da na fuskanta a rubutu shi ne a lokacin da na soma in na kai wa Furodusoshi’ ba sa karba haka ba sa kallon abin da kima kasancewar ba a sanni ba, sai da na sa juriya na yi hakuri sai gashi kuma komai ya zama labari. Haka kuma kalubalen da na fuskanta a shirya fim dina na farko ‘MALAMIN KAUNA’ gaskiya ba zai misaltu ba don ba zai fadu ba.

To batun nasarori fa?
Na samu nasarori hakika masu tarin yawa suma dai sirri ne.

Ko akwai wani fim da ka rubuta ko ka shirya wanda daga baya kake da ka sanin rubuta shi ko shirya shi sabida wasu dalilai?
MALAMIN KAUNA’ sunan fim din, ni na shirya shi Adamu Abdullahi ya rubuta, dalilin da ya sa na ji dama ban yi shi ba shi ne; na soma shi da kkarsashi amma a karshe na ji kawai na hakura da shi saboda wasu matsaloli da aka samu a dalilinsa.

A cikin fina-finan da ka rubuta ko ka shirya wanne ne ya fi shahara aka fi saninsa ya fi kuma daukar hankalin Jama’a?
Fim din shi ne ‘SIRRIN ZUCIYA’

Wadanne Jarumai ne suka fito a cikin fim din?
Ali Nuhu, Sultan Abdulrazak, Misbahu Anfara Daddy Hikima, ZPretty, Asmau Sani da dai sauransu.

Me kake son cimma game da sana’arka ta fim?
Ina so na kai matakin da duniya za ta amsa sunana haka duk abin da na yi ko na rubuta zai isar da sako a ko ina a fadin duniya, wannan shi ne burina.

Mene ne ra’ayinka game da fito wa matsayin Jarumi ko kuwa ka fi so ka tsaya a iya me rubutawa da kuma shiryawa?
Eh! Gaskiya ina da burin fara fito wa a matsayin Jarumi kuma nan ba da dadewa ba in sha Allahu zan fara fito wa a matsayin Jarumi.

Wanne abu ne ya taba faruwa da kai na farin ciki ko akasin haka wanda ba za ka taba iya mantawa da shi a rayuwarka ba?
Toh! Gaskiya abubuwan suna da yawa sai dai daya daga ciki shi ne; A kowacce rana mutane daban-daban wanda ban sani ba suna kira na su yi min fatan alkhairi da addu’a akan fim dina ‘MALAMIN KAUNA’, wannan shi ne babban abin farin cikin da na kasa mantawa da shi.

Harara

Shin Malam Abba ya na da aure ko kuwa tukunna dai?
A’a ba ni da aure tukunna dai (Dariya).

Ko akwai wadda ta taba kwanta maka a rai cikin masana’antar da har ta kai da kun fara soyayya tare?
Gaskiya babu wacce hakan ya taba faruwa tsakanin mu.

Misali wata a cikin masana’antar ta ce tana sonka za ta aure ka, shin za ka amince ka aure ta ko kuwa ba ka da ra’ayin hakan?
Eh! Zan yarda da hakan in dai ra’ayin mu ya zo daya da juna.

Wacce irin mace kake son aura?
Dariya! Na bar wa Allah zabi.

Yaushe za ka yi aure?
Aure lokaci ne duk san da ya zo mun zan yi shi, ni kaina ba na ce ga ranar ba.

Sai dai ba ka fada wa masu karatu shekarunka ba, za ka yi kamar shekara nawa yanzu?
Shekarata ashirin da takwas.

Ya ka dauki rubutun fim da kuma shirya fim a wajenka?
Su ne Ni, haka na dauki rubutu da shirya fim ba ni da kamar su, na dauke su matsayin sana’a.

Bayan wannan sana’ar da kake yi ta shirya fim da rubutawa, shin kana wata sana’ar ne?
Ba ni da wata sana’ a bayan fim.

Shin kana da Ubangida ko iyayen gida cikin masana’antar Kannywood?
Tabbas! ina da shi, Ali Rabiu Ali Daddy.

Waye Babban abokinka a cikin masana’antar Kannywood?
Babban Abokina shi ne; Salisu Yaro.

Wanne kira za ka yi ga masu kokarin shiga cikin harkar, har ma da wadanda suke ciki?
Su yi biyayya ga manyansu, sannan su yi hakuri da na gaba da su, kuma su yi abin da ya kawo su matukar suna so su yi nasara akan abin da suka sa gaba, wannan shi ne kirana ga ‘yan baya. Wadanda suke ciki kuma mu ci gaba da kyautata mu’amula kuma duk abin da zamu yi mu yi don Allah ba dan riya ba.

Harara

Wanne irin abinci da abin sha ka fi so?
Na fi son Sakwara miyar Agushi. Abin sha kuma Kunun Aya.

Wanne irin kaya ka fi son sakawa?
Na fi son Jallabiya.

Ko akwai wani kira da za ka yi wa gwamnati musamman na ganin ci gaban masana’antarku ta Kannywood?
Da a ce gwamnati za ta shiga cikin sha’anin Kannywood kuma ta saka hannun jari to da abin ya kara bunkasa ya kai duk inda ba a tunani amma wai a haka Gwamnati sai dai ta samu a jikin Kannywood wannan ba karamin abin kunya bane wallahi.

Me za ka ce ga makaranta wannan shafi na Rumbun Nishadi?
Ina godiya da jinjina a gare su Allah ya bar zumunci, su ci gaba da kasancewa da wannan shafi domin karanta gaskiya fiye da jita-jitar da za su ji a gari, domin kuwa wannan shafi kai tsaye yake kawo muku gaskiyar lamarin daya shafi duk wani dan fim ko mawaki ku ci gaba da kasancewa da wannan shafi na Rumbun Nishadi domin nishadantarwa.

Me za ka ce da ita kanta Jaridar Leadership Hausa?
Ina rokon Allah ya kara daukakata ta ci gaba da haskawa a ko ina a fadin duniyar nan.

Ko kana da wadanda za ka gaisar?
Eh! Ina gaida Ali Rabi u Ali, Salisu S. Fulani, Nasir Nid, Muhammad Dan Buzu, Ibrahim Bala, Abdul Sahir, Nasir Naba, Zahra Daimond, Humairatuh, Khadija Yobe da sauransu.

Muna godiya Malam Abba
Ni ma na gode Malama Rabi’at.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales

October 25, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
Nishadi

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?
Nishadi

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Next Post
Fayemi Ya Taya Oyebanji Murnar Lashe Zaben Gwamnan Ekiti

Fayemi Ya Taya Oyebanji Murnar Lashe Zaben Gwamnan Ekiti

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.