ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fayemi Ya Taya Oyebanji Murnar Lashe Zaben Gwamnan Ekiti

Fayemi ya ce yana da yakinin Oyebanji zai dora daga inda ya tsaya.

by Sadiq
4 years ago
Ekiti

Gwamna Kayode Fayemi na Jihar Ekiti, ya ce zaben da aka yi a ranar Asabar da ta gabata na Mista Abiodun Oyebanji na jam’iyyar APC a matsayin wanda zai gaje shi zai tabbatar da ci gaba mai dorewa a jihar.

Gwamna Fayemi ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a Ado-Ekiti mai dauke da sa hannun Mista Yinka Oyebode, babban sakataren yada labaransa.

  • Masu Son Shiga Harkar Fim Su Riki Biyayya Da Kyau – Abba Harara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Coci, Sun Kashe Mutane 3 A Kaduna

Gwamnan ya taya Oyebanji murnar fitowarsa a matsayin wanda ya lashe zaben.

ADVERTISEMENT

Oyebanji ya lashe zaben ne da kuri’u 187,057, yayin da wanda ya zo na biyu, Mista Segun Oni na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), ya samu kuri’u 82,211, sai Otunba Olabisi Kolawole na PDP da ya samu kuri’u 67,457.

Fayemi ya bayyana nasarar Oyebanji a matsayin wanda ya cancanta.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Wannan abin alfahari ne da ya dace ga mutumin da ya sadaukar da lokacinaa, kuzarinsa, basirarsa da dukiyarsa wajen ci gaban jihar nan cikin shekaru 30 da suka gabata.

“Mutanen Ekiti sun yi magana da babbar murya. Sakamakon zaben ya nuna cewa mutanen Ekiti mutane ne masu mutunci, a koyaushe suna goyon bayan shugabannin da suka yi musu hidima cikin aminci.

“Ba ni da tantama cewa zababben gwamnan zai yi wa mutanen Ekiti hidima kuma ya samar da damammaki ga sauran matasa.

“Babban yabo ya tabbata ga mutanen Jihar Ekiti na gari saboda nuna wayewa a lokacin yakin neman zabe,” inji shi.

Fayemi ya kuma jinjina wa INEC kan sabbin tsare-tsare da suka sanya aka gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da inganci, da kuma yadda hukumomin tsaro suka tabbatar da gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Ekiti
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP

Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.