• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Zanga-Zanga A Kano Na Neman Taimakon Ƙasar Rasha

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Tsaro
0
Masu Zanga-Zanga A Kano Na Neman Taimakon Ƙasar Rasha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Asabar, masu zanga-zanga a jihar Kano sun nemi shugaban ƙasar Rasha, Vladimir Putin, ya sa baki, suna daga tutar Rasha a bisa fusatar rashin kulawa da koke-kokensu daga gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu. Wannan ya faru ne a rana ta uku ta zanga-zangar tsadar rayuwa wato #EndBadGovernance da aka yi kan tsananin yunwa da talauci a Najeriya.

Zanga-zangar ta rikiɗe ta zama tashin hankali, inda ta haifar da rikici tsakanin wasu ‘yan daba da jami’an tsaro, wanda ya janyo mutuwar mutane da dama da raunata wasu.

  • Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
  • Tsadar Rayuwa: Atiku Ya Yi Allah Wadai Da Harbin Masu Zanga-zanga 

Shaidu sun ruwaito cewa rikicin ya fara ne lokacin da matasa suka saɓa dokar hana fita da jihar ta ƙaƙaba don ci gaba da zanga-zangar a yankunan Rijiyar Lemo, da Kurna zuwa Bachirawa, da Kofar Nasarawa, da Unguwa Uku.

Abdulkadir Musa, mazaunin Rijiyar Lemo, ya bayyana cewa an harbe a ƙalla mutane takwas, ciki har da mata da yara, tare da tabbatar da mutuwar tsohuwa da wasu mutane uku. An ce ƴan dabar sun yi ƙoƙarin fasa shaguna suna fakewa da zanga-zangar yunwa, wanda ya haifar da ƙarin tashin hankali da raunuka.

Masu amfani da kafofin sada zumunta sun yi wallafe wallafe game da tarzomar, suna nuna yadda ƴansanda suka yi amfani da ƙarfi don tarwatsa masu zanga-zangar.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

Rundunar Ƴansanda ta jihar Kano ba ta yi ƙarin haske kan rahotannin kisan ba, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta. Ƙoƙarin tuntubar mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, bai yi nasara ba saboda ba a iya samun sa ta waya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Sassan Ba Da Hidima

Next Post

Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

2 days ago
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

1 week ago
Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Tsaro

Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice

1 week ago
Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci
Tsaro

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

1 week ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi
Tsaro

Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2
Tsaro

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

2 weeks ago
Next Post
Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

Jami’in Zimbabwe Ya Yabawa Kamfanin Kasar Sin Da Ya Goyi Bayan Ajandar Bunkasa Masana’antun SADC

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Zanga-zanga

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.