• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
6 months ago
in Adon Gari
0
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashiya Zainab matashiya ‘yar asalin Jihar Hadejia Jihar Jigawa, daliba a fannin lafiya, ta bayyana wa wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM, yadda take gudanar da harkokin karatunta jin dadinsa da kuma kalubalensa, ciki har da shawarar da bai wa mata na samnun mafita ta fuskar karatu. Kamar dai yadda za ku karanta kamar haka.

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Suna na Zainab Ahmad Ibrahim, an haife ni a garin Hadeja, na yi magarantar Firamare a garin Hadeja a Garko Community, na yi Sakandire a Unguwar Sarki duk a garin Hadeja dake Jihar Jigawa daga nan na tafi Babura na fara karatun Difloma, a yanzu haka ina can.

 

Matar aure ce?

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

A’a ba ni da aure

 

Malama Zainab kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

A gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a da nake yi sai dai karatu shi na sa a gaba, domin babban burina na ga na kammala karatuna babu wata matsala shi ya sa ba na son hada karatu da komai sai dai idan na gama.

 

Me kike karantawa?

Ina karatu a bangaran sanin cututtuka ne wato ‘Epidemiology and disease control’, kuma abin da ya sa na zabi wannan bangaren saboda ina da sha’awar sanin cututtuka da yadda za’a yi maganin zuwanta idan ya samu

 

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

To ni dai a gaskiya babu wani abin da ya ja hankalina har nake sha’awar wannan karatu tun ina karama, idan na ga ko na ji an ce cuta ta kama mutum har ta kai ga ya rasa rayuwarsa sai na yi ta tunanin ita wannan cutar meye maganinta ko ba ta da magani ko ba a san maganin bane, sai na ji an ce ai Allah kafin ya saukar da cuta sai da ya fara saukar da magani sai na yi ta tunanin haka, to wannan shi ne dalilina na yin karatu a wannan bangaren.

 

Wanne irin kalubale kike fuskanta a karatunki?

Gaskiya kalubalen da na fuskanta shi ne akan dakin kwana, na sha wahala sosai kafin na samu kasancewar ni ba ‘yar gari bace, sannan kuma gaskiya bamu da ‘yan uwa a garin saboda haka ban san kowa ba gani kuma sabuwar daliba, ‘yan makarantar ma ban san su ba ballantana wata na dan yi sukwatin dina, amma Alhamdu lillahi da haka na mamuka cikin dakin kwanan domin sanin mutane, a haka Allah ya hada ni da wata ta yi sukwatin dina har na samu nawa nima.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Gaskiya na samu nasarori game da karatuna sosai, sai dai na yi ta gode wa Allah Alhamdu lillahi, saboda ban taba samun wata matsala ba, na shiga waje ma na zauna da mutane lafiya shima wannan babbar nasara ce.

 

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da ya fi faranta min rai game da karatuna shi ne, yadda mutane suke mini kallon daraja ko a waje ana girmama ni sosai kuma makaranta ma kowa yana girmama ni mutane suna ganin daraja ta, to idan na ga yadda ake min a makaranta wannan yana faranta min rai kasancewa za ki ga wasu an samu akasin haka.

 

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rinka tunawa da ni ta wajen kamun kaina da haba-haba da mutane da wasa da dariya.

 

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Idan aka ce Allah ya jikan mahaifina to ina jin dadin wannan addu’ar gaskiya kasancewa mahaifina ba ya raye.

 

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Gaskiya ina samun goyon bayan mahaifiyata da ‘yan uwana sosai, saboda su suka goya min bayan yin karatuna na gode musu sasai Allah ya saka da alkhairi.

 

Kawaye fa?

Suma ina godiya a gare su.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Kayan sawa ina son doguwar riga ta atamfa, kayan kwalliya kuma hoda kadai.

 

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

To gaskiya abin da zan iya cewa shi ne, mata a dage da karatu domin temakawa rayuwarku da ta ‘ya’yanku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ta Zanta Da Shugaban Kasar Brazil

Next Post

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

Related

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

1 week ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Tsokaci A Kan Rayuwar Sabuwar Karamar Ministar Ilimi
Adon Gari

Tsokaci A Kan Rayuwar Sabuwar Karamar Ministar Ilimi

6 months ago
Next Post
An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

LABARAI MASU NASABA

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.