• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
8 months ago
in Adon Gari
0
Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashiya Zainab matashiya ‘yar asalin Jihar Hadejia Jihar Jigawa, daliba a fannin lafiya, ta bayyana wa wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM, yadda take gudanar da harkokin karatunta jin dadinsa da kuma kalubalensa, ciki har da shawarar da bai wa mata na samnun mafita ta fuskar karatu. Kamar dai yadda za ku karanta kamar haka.

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Suna na Zainab Ahmad Ibrahim, an haife ni a garin Hadeja, na yi magarantar Firamare a garin Hadeja a Garko Community, na yi Sakandire a Unguwar Sarki duk a garin Hadeja dake Jihar Jigawa daga nan na tafi Babura na fara karatun Difloma, a yanzu haka ina can.

 

Matar aure ce?

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

A’a ba ni da aure

 

Malama Zainab kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

A gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a da nake yi sai dai karatu shi na sa a gaba, domin babban burina na ga na kammala karatuna babu wata matsala shi ya sa ba na son hada karatu da komai sai dai idan na gama.

 

Me kike karantawa?

Ina karatu a bangaran sanin cututtuka ne wato ‘Epidemiology and disease control’, kuma abin da ya sa na zabi wannan bangaren saboda ina da sha’awar sanin cututtuka da yadda za’a yi maganin zuwanta idan ya samu

 

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

To ni dai a gaskiya babu wani abin da ya ja hankalina har nake sha’awar wannan karatu tun ina karama, idan na ga ko na ji an ce cuta ta kama mutum har ta kai ga ya rasa rayuwarsa sai na yi ta tunanin ita wannan cutar meye maganinta ko ba ta da magani ko ba a san maganin bane, sai na ji an ce ai Allah kafin ya saukar da cuta sai da ya fara saukar da magani sai na yi ta tunanin haka, to wannan shi ne dalilina na yin karatu a wannan bangaren.

 

Wanne irin kalubale kike fuskanta a karatunki?

Gaskiya kalubalen da na fuskanta shi ne akan dakin kwana, na sha wahala sosai kafin na samu kasancewar ni ba ‘yar gari bace, sannan kuma gaskiya bamu da ‘yan uwa a garin saboda haka ban san kowa ba gani kuma sabuwar daliba, ‘yan makarantar ma ban san su ba ballantana wata na dan yi sukwatin dina, amma Alhamdu lillahi da haka na mamuka cikin dakin kwanan domin sanin mutane, a haka Allah ya hada ni da wata ta yi sukwatin dina har na samu nawa nima.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Gaskiya na samu nasarori game da karatuna sosai, sai dai na yi ta gode wa Allah Alhamdu lillahi, saboda ban taba samun wata matsala ba, na shiga waje ma na zauna da mutane lafiya shima wannan babbar nasara ce.

 

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da ya fi faranta min rai game da karatuna shi ne, yadda mutane suke mini kallon daraja ko a waje ana girmama ni sosai kuma makaranta ma kowa yana girmama ni mutane suna ganin daraja ta, to idan na ga yadda ake min a makaranta wannan yana faranta min rai kasancewa za ki ga wasu an samu akasin haka.

 

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rinka tunawa da ni ta wajen kamun kaina da haba-haba da mutane da wasa da dariya.

 

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Idan aka ce Allah ya jikan mahaifina to ina jin dadin wannan addu’ar gaskiya kasancewa mahaifina ba ya raye.

 

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Gaskiya ina samun goyon bayan mahaifiyata da ‘yan uwana sosai, saboda su suka goya min bayan yin karatuna na gode musu sasai Allah ya saka da alkhairi.

 

Kawaye fa?

Suma ina godiya a gare su.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Kayan sawa ina son doguwar riga ta atamfa, kayan kwalliya kuma hoda kadai.

 

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

To gaskiya abin da zan iya cewa shi ne, mata a dage da karatu domin temakawa rayuwarku da ta ‘ya’yanku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Ta Zanta Da Shugaban Kasar Brazil

Next Post

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

1 month ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

2 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

5 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

7 months ago
Next Post
An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.