ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
2 years ago
Mata

Matashiya Zainab matashiya ‘yar asalin Jihar Hadejia Jihar Jigawa, daliba a fannin lafiya, ta bayyana wa wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM, yadda take gudanar da harkokin karatunta jin dadinsa da kuma kalubalensa, ciki har da shawarar da bai wa mata na samnun mafita ta fuskar karatu. Kamar dai yadda za ku karanta kamar haka.

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Suna na Zainab Ahmad Ibrahim, an haife ni a garin Hadeja, na yi magarantar Firamare a garin Hadeja a Garko Community, na yi Sakandire a Unguwar Sarki duk a garin Hadeja dake Jihar Jigawa daga nan na tafi Babura na fara karatun Difloma, a yanzu haka ina can.

ADVERTISEMENT

 

Matar aure ce?

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

A’a ba ni da aure

 

Malama Zainab kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa a gaba?

A gaskiya yanzu ba ni da wata sana’a da nake yi sai dai karatu shi na sa a gaba, domin babban burina na ga na kammala karatuna babu wata matsala shi ya sa ba na son hada karatu da komai sai dai idan na gama.

 

Me kike karantawa?

Ina karatu a bangaran sanin cututtuka ne wato ‘Epidemiology and disease control’, kuma abin da ya sa na zabi wannan bangaren saboda ina da sha’awar sanin cututtuka da yadda za’a yi maganin zuwanta idan ya samu

 

Me ya ja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun?

To ni dai a gaskiya babu wani abin da ya ja hankalina har nake sha’awar wannan karatu tun ina karama, idan na ga ko na ji an ce cuta ta kama mutum har ta kai ga ya rasa rayuwarsa sai na yi ta tunanin ita wannan cutar meye maganinta ko ba ta da magani ko ba a san maganin bane, sai na ji an ce ai Allah kafin ya saukar da cuta sai da ya fara saukar da magani sai na yi ta tunanin haka, to wannan shi ne dalilina na yin karatu a wannan bangaren.

 

Wanne irin kalubale kike fuskanta a karatunki?

Gaskiya kalubalen da na fuskanta shi ne akan dakin kwana, na sha wahala sosai kafin na samu kasancewar ni ba ‘yar gari bace, sannan kuma gaskiya bamu da ‘yan uwa a garin saboda haka ban san kowa ba gani kuma sabuwar daliba, ‘yan makarantar ma ban san su ba ballantana wata na dan yi sukwatin dina, amma Alhamdu lillahi da haka na mamuka cikin dakin kwanan domin sanin mutane, a haka Allah ya hada ni da wata ta yi sukwatin dina har na samu nawa nima.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

Gaskiya na samu nasarori game da karatuna sosai, sai dai na yi ta gode wa Allah Alhamdu lillahi, saboda ban taba samun wata matsala ba, na shiga waje ma na zauna da mutane lafiya shima wannan babbar nasara ce.

 

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da ya fi faranta min rai game da karatuna shi ne, yadda mutane suke mini kallon daraja ko a waje ana girmama ni sosai kuma makaranta ma kowa yana girmama ni mutane suna ganin daraja ta, to idan na ga yadda ake min a makaranta wannan yana faranta min rai kasancewa za ki ga wasu an samu akasin haka.

 

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ina so mutane su rinka tunawa da ni ta wajen kamun kaina da haba-haba da mutane da wasa da dariya.

 

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Idan aka ce Allah ya jikan mahaifina to ina jin dadin wannan addu’ar gaskiya kasancewa mahaifina ba ya raye.

 

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Gaskiya ina samun goyon bayan mahaifiyata da ‘yan uwana sosai, saboda su suka goya min bayan yin karatuna na gode musu sasai Allah ya saka da alkhairi.

 

Kawaye fa?

Suma ina godiya a gare su.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Kayan sawa ina son doguwar riga ta atamfa, kayan kwalliya kuma hoda kadai.

 

A karshe wace irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

To gaskiya abin da zan iya cewa shi ne, mata a dage da karatu domin temakawa rayuwarku da ta ‘ya’yanku.

Mata
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
Mata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.