• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Dage Da Tsare Mutuncin Kai – Zainab Muhammad

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Mata A Dage Da Tsare Mutuncin Kai – Zainab Muhammad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

ZAINAB MUHAMAD mai neman ilimi kuma ‘yar kasuwancin sayar da kayan kamshi na mata ‘yar asalin Garin Hadejia ta yi wa shafi Adon Gari karin haske kan yadda ta tsinci kanta a harkar kasuwaci wanda ta ce ta samu rufin asiri sosai a cikinta, sannan ta yi kira ga mata da su koyi sana’a domin su tsira da mutuncinsu, kamar yadda za ku ji a wannan hira da wakiliyarmu BILIKSU TIJJANI KASSIM.

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Suna na Zainab Muhammad Sambo, ni cikakkiyar ‘ya Hadejia ce an haife ni a Garin Hadejia a shekara ta 1997 a Unguwar Wuriwa, na yi makaranta a Garin Hadejia

Shin Zainab matar aure ce?

A’a ni ba matar aure bace muna niyya in sha Allahu.

‘Yar kasuwa ce ko ma’aikaciya?

A a ni ba ma’aikaciya bace, ina dan taba kasuwanci haka-kadan dai wanda ba’a rasa ba.

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Kayan kamshi nake sayarwa

Shin me kasuwancin naki ya kunsa?

Kamar turaren wuta, Humura da duk nau’ika na kayan kamshi da sauransu.

To ke kuwa me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwanci?

Saboda ni ma’abociyar san kamshi ce.

Me ye matakin karatunki?

Na gama Difiloma.

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

Kalubalan da na fuskanta akwai ranar da wata ta sani na hada mata turaren wuta amma ba ta saya ba shi ne kalubale na da na taba fuskanta, saboda abin ya bani haushi kin san dai yadda hadin turare yake da wahala ka kwana kana yi sai da na gama ba ta kara magana ba.

Zuwa yanzu wanne irin nasarori kika cimma?

Na samu nasarori da dama bikin kawayena da taron makaranta duk da sana’ ata nake yi har na tallafa wa mabukata

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Alhamdu lillah idan na yi turare a ce ya yi dadi ana so wannan yana faranta min rai ina jin dadin haka sosai.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Ta hanyar intanet kamar whatsapp, facebook, instagram, da dai sauransu.

Dame kike so mutane su rika tunawa dake?

Ina so mutane su rika tunawa da ni a kan kamshina da kuma fara’a ta da wasa da dariya.

Ga karatu, ga kuma kila kina taya mama ayyukan gida, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Kome nawa a tsare yake komai na ba shi lokacinsa.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

In aka min addu’ar Allah ya jikan mahaifina ina jin dadi sosai

Wane irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

 Alhamdu lillah ina samun goyan baya dari bisa dari a wurin iyayena da ‘yan uwana babu abin da zan ce musu sai godiya da kuma addu’ar Allah ya saka musu da alkhairi.

Kawaye fa?

Ni ban da kawaye, ‘yan uwana su ne kawayena

Me kika fi so cikin kayan sawa fa kayan kwalliya?

Ina son leshi da doguwar riga ta komai kayan kwalliya kuma ba na son na ga idona babu kwalli.

A karshe wace irin shawara za ki bawa ‘yan uwanki mata?

Shawarata ga mata ‘yan uwana su dage su nemi sana’a kuma su tsare mutumcinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariMataMutuncin Kai
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kori Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Zamfara Tukur Danfulani Daga Jamiyyar

Next Post

Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila’in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 weeks ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

1 month ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

4 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

5 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

6 months ago
Next Post
Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila’in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila'in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

LABARAI MASU NASABA

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

June 16, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev

Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev

June 16, 2025
Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Bunkasar Masana’antu A Nahiyar Afirka, In Ji Wani Masanin Tattalin Arziki

Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Bunkasar Masana’antu A Nahiyar Afirka, In Ji Wani Masanin Tattalin Arziki

June 16, 2025
Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

June 16, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.