ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

by Aisha Seyoji
2 years ago
Mata marayu

Aisha Seyoji matashiyar ‘yar kasuwa kuma magidancinya mai kokarin neman na kanta ta shawarci mata da ke zaune a gidajen mazajensu da su kyautata hakuri a zamantakewar aure, tare da neman na kansu domin tsira da mutuncinsu. Ta  ba da wannan shawara ce a tattaunawarsu da wakiliyar LEADERSHIP BILIKSU TIJJANI KASSIM. Baya ga haka ta bayyana irin nasarar da ta samu a kasuwancinta, ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

Da farko masu karatu za su su ji sunanki da kuma dan takaitaccen tarihinki

Sunana Aisha Seyoji. An haife ni a Garin Gombe, na yi Firamare da jami’a duka a Bauchi.

ADVERTISEMENT

 

Yaya batun aure da iyali a warinki?

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ina da aure da ‘ya’yana uku.

 

A halin yanzu masu karatu na bukatar su san shin kina aiki ne ko karatu ko kuma sana’a, wane mataki kike ko zaman gida kike?

Toh Alhamdulillah, Ina aiki, ina kasuwanci, a kasuwancin ina saida kusan duk wani nau’i na abin da ya shafi kayan kamshi.

 

Shin ko za mu iya sanin abin da ya jawo hankalinki kan wannan sana’a?

Abin da ya ja hankalina na fara wannan sana’a ta kayan kamshi, gaskiya na kasance ma’abociyar son turare kama daga na jiki, na kaya da na gida. Wannan soyayya da nake da ita ga kamshi ya sa na fara sha’awar sana’ar kayan kamshi, Allah cikin ikonsa na hadu da wata baiwar Allah a Kano wanda itama tana kasuwanci kuma kusan komai tana saidawa ciki har da turaruka, nan dai na nuna mata sha’awata na son sanin yadda abin yake, daga nan ta fara nuna min, sannu a hankali kuma yanzu cikin hukuncin Allah sai gashi ina da shago nawa na kaina wanda ake saida kayan kamshi.

 

Ta wacce hanya kikebi wajen tallata sana’aki?

Eh to ba wata hanya ba ne sai ta intanet, a gaskiya na fi saida kayana ta Whatsapp, Instagram, Facebook da dai sauransu, sai kuma mutanena haka na gida da waje.

 

Shin ko akwai wata hanya da kike ganin gwamnati za ta iya shigowa cikin wannan sana’a taki ta tallafa domin a samu karin masu yi don Samar da aikinyi?

Eh sosai ma kuwa, gwamnati za ta iya shiga ciki ta taimaka, misali a ce irin shirye-shiryen gwamnati da suke yi na ‘Empowerment’ wato tallafi da ake ba wa jama’a domin kama sana’a su dogara da kansu.

 

Ko za ki bayyana wa mai karatu wani abu da ya taba faruwa da ke a rayuwa na farin ciki ko akasinsa da ba za ki taba mantawa ba?

Alhamdulillah gaskiya abubuwa na farin ciki da yawa sun faru wanda ba abin da zance wa Allah sai dai godiya. Rasuwar mahaifiyata shi ne ba zan taba mantawa da shi ba.

 

Ko kina da shawara da za ki ba wa mutane game da sha’anin rayuwa ta yau da kullum wanda idan suka yi koyi ko amfani da ita, rayuwa za ta inganta?

Shawarata ga al’umma itace, a duk inda muka tsinci kanmu mu rika tuna Allah farko, mu rike gaskiya da amana, tausayi da jinkan na kasa damu.

 

Idan muka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a yanzu, me za ki ce wa iyaye a kan muhimmancin tarbiyya kasancewar su kansu wadannan ‘ya’ya amana ce Ubangiji ya ba mu kuma zai tambaye mu a kan yadda muka tafiyar da su?

Tabbas iyaye mu ji tsoron Allah, mu sani cewa ‘ya’ya wata amana ne da ubangiji ya bamu kuma tabbas zai tambaye mu ta yadda muka tarbiyantar da su, mu yi kokari mu cire son zuciya mu rika gaya wa ‘ya’yanmu gaskiya ta hanyar nasiha da tunatarwa, mu koya musu sanin muhimmanci gaskiya, hakuri, juriya tawakkali, da kuma dogaro da kai.

 

Wace shawara za ki ba wa matan aure akan rayuwar aure duba ga irin zamanin da muke ciki?

Gare mu ‘yan uwa mata. Hakuri, hakuri mu kara akan wanda muke yi, mu kasance masu juriya da wadatar zuciya sannan uwa uba abin da ya fi muhimmanci ita ce addu’a.

A karshe zan mika sakon godiya ta musamman ga wannan gidan jarida na LEADERSHIP da ya bani damar kasancewa tare da ita a wannan tattaunawa, jinjina ta musamman gareki Hajiya Bilkisu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama’a

Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama'a

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.