• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

by Aisha Seyoji
1 year ago
in Adon Gari
0
Mata marayu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Seyoji matashiyar ‘yar kasuwa kuma magidancinya mai kokarin neman na kanta ta shawarci mata da ke zaune a gidajen mazajensu da su kyautata hakuri a zamantakewar aure, tare da neman na kansu domin tsira da mutuncinsu. Ta  ba da wannan shawara ce a tattaunawarsu da wakiliyar LEADERSHIP BILIKSU TIJJANI KASSIM. Baya ga haka ta bayyana irin nasarar da ta samu a kasuwancinta, ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

Da farko masu karatu za su su ji sunanki da kuma dan takaitaccen tarihinki

Sunana Aisha Seyoji. An haife ni a Garin Gombe, na yi Firamare da jami’a duka a Bauchi.

 

Yaya batun aure da iyali a warinki?

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

Ina da aure da ‘ya’yana uku.

 

A halin yanzu masu karatu na bukatar su san shin kina aiki ne ko karatu ko kuma sana’a, wane mataki kike ko zaman gida kike?

Toh Alhamdulillah, Ina aiki, ina kasuwanci, a kasuwancin ina saida kusan duk wani nau’i na abin da ya shafi kayan kamshi.

 

Shin ko za mu iya sanin abin da ya jawo hankalinki kan wannan sana’a?

Abin da ya ja hankalina na fara wannan sana’a ta kayan kamshi, gaskiya na kasance ma’abociyar son turare kama daga na jiki, na kaya da na gida. Wannan soyayya da nake da ita ga kamshi ya sa na fara sha’awar sana’ar kayan kamshi, Allah cikin ikonsa na hadu da wata baiwar Allah a Kano wanda itama tana kasuwanci kuma kusan komai tana saidawa ciki har da turaruka, nan dai na nuna mata sha’awata na son sanin yadda abin yake, daga nan ta fara nuna min, sannu a hankali kuma yanzu cikin hukuncin Allah sai gashi ina da shago nawa na kaina wanda ake saida kayan kamshi.

 

Ta wacce hanya kikebi wajen tallata sana’aki?

Eh to ba wata hanya ba ne sai ta intanet, a gaskiya na fi saida kayana ta Whatsapp, Instagram, Facebook da dai sauransu, sai kuma mutanena haka na gida da waje.

 

Shin ko akwai wata hanya da kike ganin gwamnati za ta iya shigowa cikin wannan sana’a taki ta tallafa domin a samu karin masu yi don Samar da aikinyi?

Eh sosai ma kuwa, gwamnati za ta iya shiga ciki ta taimaka, misali a ce irin shirye-shiryen gwamnati da suke yi na ‘Empowerment’ wato tallafi da ake ba wa jama’a domin kama sana’a su dogara da kansu.

 

Ko za ki bayyana wa mai karatu wani abu da ya taba faruwa da ke a rayuwa na farin ciki ko akasinsa da ba za ki taba mantawa ba?

Alhamdulillah gaskiya abubuwa na farin ciki da yawa sun faru wanda ba abin da zance wa Allah sai dai godiya. Rasuwar mahaifiyata shi ne ba zan taba mantawa da shi ba.

 

Ko kina da shawara da za ki ba wa mutane game da sha’anin rayuwa ta yau da kullum wanda idan suka yi koyi ko amfani da ita, rayuwa za ta inganta?

Shawarata ga al’umma itace, a duk inda muka tsinci kanmu mu rika tuna Allah farko, mu rike gaskiya da amana, tausayi da jinkan na kasa damu.

 

Idan muka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a yanzu, me za ki ce wa iyaye a kan muhimmancin tarbiyya kasancewar su kansu wadannan ‘ya’ya amana ce Ubangiji ya ba mu kuma zai tambaye mu a kan yadda muka tafiyar da su?

Tabbas iyaye mu ji tsoron Allah, mu sani cewa ‘ya’ya wata amana ne da ubangiji ya bamu kuma tabbas zai tambaye mu ta yadda muka tarbiyantar da su, mu yi kokari mu cire son zuciya mu rika gaya wa ‘ya’yanmu gaskiya ta hanyar nasiha da tunatarwa, mu koya musu sanin muhimmanci gaskiya, hakuri, juriya tawakkali, da kuma dogaro da kai.

 

Wace shawara za ki ba wa matan aure akan rayuwar aure duba ga irin zamanin da muke ciki?

Gare mu ‘yan uwa mata. Hakuri, hakuri mu kara akan wanda muke yi, mu kasance masu juriya da wadatar zuciya sannan uwa uba abin da ya fi muhimmanci ita ce addu’a.

A karshe zan mika sakon godiya ta musamman ga wannan gidan jarida na LEADERSHIP da ya bani damar kasancewa tare da ita a wannan tattaunawa, jinjina ta musamman gareki Hajiya Bilkisu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Kara Kaimin Sintiri A Arewa Maso Gabas Domin Dakile Karancin Kayan Abinci

Next Post

Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama’a

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

6 days ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

3 weeks ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

3 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

5 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

5 months ago
Next Post
Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama’a

Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama'a

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.