• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

by Aisha Seyoji
2 years ago
in Adon Gari
0
Mata marayu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Seyoji matashiyar ‘yar kasuwa kuma magidancinya mai kokarin neman na kanta ta shawarci mata da ke zaune a gidajen mazajensu da su kyautata hakuri a zamantakewar aure, tare da neman na kansu domin tsira da mutuncinsu. Ta  ba da wannan shawara ce a tattaunawarsu da wakiliyar LEADERSHIP BILIKSU TIJJANI KASSIM. Baya ga haka ta bayyana irin nasarar da ta samu a kasuwancinta, ga dai yadda hirar tasu ta kasance:

Da farko masu karatu za su su ji sunanki da kuma dan takaitaccen tarihinki

Sunana Aisha Seyoji. An haife ni a Garin Gombe, na yi Firamare da jami’a duka a Bauchi.

 

Yaya batun aure da iyali a warinki?

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Ina da aure da ‘ya’yana uku.

 

A halin yanzu masu karatu na bukatar su san shin kina aiki ne ko karatu ko kuma sana’a, wane mataki kike ko zaman gida kike?

Toh Alhamdulillah, Ina aiki, ina kasuwanci, a kasuwancin ina saida kusan duk wani nau’i na abin da ya shafi kayan kamshi.

 

Shin ko za mu iya sanin abin da ya jawo hankalinki kan wannan sana’a?

Abin da ya ja hankalina na fara wannan sana’a ta kayan kamshi, gaskiya na kasance ma’abociyar son turare kama daga na jiki, na kaya da na gida. Wannan soyayya da nake da ita ga kamshi ya sa na fara sha’awar sana’ar kayan kamshi, Allah cikin ikonsa na hadu da wata baiwar Allah a Kano wanda itama tana kasuwanci kuma kusan komai tana saidawa ciki har da turaruka, nan dai na nuna mata sha’awata na son sanin yadda abin yake, daga nan ta fara nuna min, sannu a hankali kuma yanzu cikin hukuncin Allah sai gashi ina da shago nawa na kaina wanda ake saida kayan kamshi.

 

Ta wacce hanya kikebi wajen tallata sana’aki?

Eh to ba wata hanya ba ne sai ta intanet, a gaskiya na fi saida kayana ta Whatsapp, Instagram, Facebook da dai sauransu, sai kuma mutanena haka na gida da waje.

 

Shin ko akwai wata hanya da kike ganin gwamnati za ta iya shigowa cikin wannan sana’a taki ta tallafa domin a samu karin masu yi don Samar da aikinyi?

Eh sosai ma kuwa, gwamnati za ta iya shiga ciki ta taimaka, misali a ce irin shirye-shiryen gwamnati da suke yi na ‘Empowerment’ wato tallafi da ake ba wa jama’a domin kama sana’a su dogara da kansu.

 

Ko za ki bayyana wa mai karatu wani abu da ya taba faruwa da ke a rayuwa na farin ciki ko akasinsa da ba za ki taba mantawa ba?

Alhamdulillah gaskiya abubuwa na farin ciki da yawa sun faru wanda ba abin da zance wa Allah sai dai godiya. Rasuwar mahaifiyata shi ne ba zan taba mantawa da shi ba.

 

Ko kina da shawara da za ki ba wa mutane game da sha’anin rayuwa ta yau da kullum wanda idan suka yi koyi ko amfani da ita, rayuwa za ta inganta?

Shawarata ga al’umma itace, a duk inda muka tsinci kanmu mu rika tuna Allah farko, mu rike gaskiya da amana, tausayi da jinkan na kasa damu.

 

Idan muka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa a yanzu, me za ki ce wa iyaye a kan muhimmancin tarbiyya kasancewar su kansu wadannan ‘ya’ya amana ce Ubangiji ya ba mu kuma zai tambaye mu a kan yadda muka tafiyar da su?

Tabbas iyaye mu ji tsoron Allah, mu sani cewa ‘ya’ya wata amana ne da ubangiji ya bamu kuma tabbas zai tambaye mu ta yadda muka tarbiyantar da su, mu yi kokari mu cire son zuciya mu rika gaya wa ‘ya’yanmu gaskiya ta hanyar nasiha da tunatarwa, mu koya musu sanin muhimmanci gaskiya, hakuri, juriya tawakkali, da kuma dogaro da kai.

 

Wace shawara za ki ba wa matan aure akan rayuwar aure duba ga irin zamanin da muke ciki?

Gare mu ‘yan uwa mata. Hakuri, hakuri mu kara akan wanda muke yi, mu kasance masu juriya da wadatar zuciya sannan uwa uba abin da ya fi muhimmanci ita ce addu’a.

A karshe zan mika sakon godiya ta musamman ga wannan gidan jarida na LEADERSHIP da ya bani damar kasancewa tare da ita a wannan tattaunawa, jinjina ta musamman gareki Hajiya Bilkisu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Kara Kaimin Sintiri A Arewa Maso Gabas Domin Dakile Karancin Kayan Abinci

Next Post

Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama’a

Related

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

3 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

5 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Next Post
Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama’a

Jigawa Za Ta Ci Gaba Da Rike Matsayinta Na Jihar Da Alummarta Ba Sa Yin Bahaya A Bainar Jama'a

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.