Wasu mata daga unguwar Oke-Ere da ke Ƙaramar Hukumar Yagba ta Yamma a Jihar Kogi, sun yi zanga-zanga domin nuna damuwa kan yawaitar sace-sace da rashin tsaro a yankin.
Wata majiya daga yankin ta bayyana cewa zanga-zangar ta biyo bayan iƙirarin wani tsohon ɗan bindiga da ya tuba, inda ya bayyana cewa wasu ‘yan yankin suna da hannun masj garkuwa da mutane, lamarin da ya fusata matan yankin.
- Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 12 Cikin Jerin Wadanda Ta Dakatar Da Fitar Musu Da Wasu Kayayyaki Daga Kasar Sin
- Yadda Kasashen Afirka Za Su Iya Rage Illar Harajin Amurka
Sai dai Shugaban ƙaramar hukumar, Tosin Olokun, ya musanta wannan zargi, inda ya ce abin da ya faru ba zanga-zanga ba ce, illa wata addu’a ce da ake yi a kowace shekara domin zaman lafiya.
Ya ce an samu izini daga wajen sarakunan gargajiya kafin fitowar matan, kuma an shirya lamarin ne da sanin Elere na Ere, shugaban al’ummar yankin.
A cewarsa, wannan taro na mata yana daga cikin al’adar shekara-shekara da ake gudanarwa domin neman zaman lafiya da kuma yin addu’o’i na fatan alheri ga al’umma.
Yankin Kogi ta Yamma na fama da matsalar tsaro, inda aka ruwaito wasu mazauna garin Oduape a Ƙaramar Hukumar Kabba Bunu sun gudanar da zanga-zanga a bara domin nuna fargabarsu game da yawaitar sace-sace da kashe-kashe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp