Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Ondo, Abayomi Akinruntan, da Shugaban Masu Rinjaye, Emmanuel Ogunmolasuyi, sun sauka daga muƙamansu.
Akinruntan, ɗan sarkin Ugbo, Oba Frederick Obateru Akinruntan daga ƙaramar hukumar Ilaje, bai bayyana dalilin saukarsa ba.
- Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
- Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
A cikin wasiƙar saukarsa, ya gode wa ‘yan majalisar bisa yadda suka zaɓe shi a matsayin mataimakin kakakin majalisar.
Kodayake ba a bayyana a hukumance dalilin saukarsa ba, wasu majiyoyi sun ce saukarsa na da nasaba da harkokin siyasa.
Wasu na ganin hakan na da alaƙa da kasancewarsa daga ƙaramar hukuma ɗata da Gwamna Lucky Aiyedatiwa.
Wasu kuma sun ce akwai rashin jituwa tsakanin Gwamnan da mahaifinsa, Oba Akinruntan.
Bayan saukar Akinruntan, an zaɓi Ololade Gbegudu daga Okitipupa a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.
Gbegudu, mai shekara 42, ya riƙe muƙamin shugaban kwamitin tsaro da ci gaban al’umma a majalisar kafin wannan sabon muƙamin.
Oluwatoyin James daga Akoko ta Arewa Maso Gabas ne, ya ayyana sunansa, yayin da Chris Aiyebusiwa daga Okitipupa I ya mara masa baya.
Haka kuma, tsohon jagoran majalisar, Ogunmolasuyi daga Owo I, ya sauya wajen aiki da Olatunji Oshati daga mazaɓar Ose, wanda yanzu shi ne sabon shugaban masu rinjaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp