Mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng, ya halarci babban taron MDD kan tekuna karo na 3, wanda aka gudanar a kasar Faransa, tsakanin ranakun 8 zuwa 9 ga watan nan da muke ciki, bisa gayyatar da aka yi masa.
A jawabin da ya gabatar yayin taron muhawara da aka yi, Han Zheng ya ce, a bana, aka cika shekaru 80 da kafuwar MDD, don haka zai fi kyau a yi amfani da wannan dama ta gudanar da babban taron MDD kan tekuna, wajen daidaita aikin kare da raya dauwamammen ci gaban albarkatun tekuna, ta yadda za a gina makomar bil Adama ta bai daya.
Ya kara da cewa, da farko, ya kamata a kafa yanayin zaman lafiya da tsaron tekuna cikin hadin gwiwa. Sa’an nan kuma, a inganta aikin amfani da albarkatun tekuna domin tallafawa juna. Haka kuma, ya kamata a karfafa wayewar kai da mu’amala kan harkoki masu nasaba da tekuna. A karshe kuma, ya kamata a dukufa wajen kiyaye tsabtar tekuna.
Bugu da kari, ya ce, kasar Sin za ta karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kungiyoyin kasa da kasa da abin ya shafa, ta hanyar amfani da Asusun raya kasashen duniya da hadin gwiwar dake tsakanin kasashe masu tasowa, domin gudanar da ayyukan da suka shafi tekuna, yayin raya harkokin da abin ya shafa ta hanyoyin kare muhalli. Haka kuma, kasar Sin tana fatan ganin aiwatarwar da yarjejeniyar kiyaye nau’o’in halittun tekuna cikin sauri, kuma bisa dukkan fannoni.
A yayin taron, Han Zheng ya kuma gana da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, da babban magatakardan MDD Antonio Guterres. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp