• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara

by Hussein Yero
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon matsalar ruwan sha da ta addabi Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, yanzu haka yara ne suka mutu sakamakon jigilar ruwan sha a kwale-kwale.

Yara 12 sun kuma nutse a cikin ruwa ba tare da an gano su ba a Gulbin Tulukawa da ke jihar.

  • Sauyin Gwamnati: Wainar Da Ake Toyawa A Jihohin  Da ‘Yan Adawa Za Su Karbi Mulki
  • Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Daya daga cikin wanda suka tsamo gawarwakin yaran, Sani Aliyu, ya bayyana wa manema labarai cewa, kwale-kwale ya nutse ne bayan yaran sun dauko ruwa daga hayin labuna inda suke samo ruwan wajen masu noman rani da suka gina rijiya da suke amfani da ita.

“Bayan sun loda jarkunan ruwa da su yaran maza da mata a kwale-kwale su na tsakiyar koramar sai kwale-kwalen ya yi ta tangal-tangal, inda take su kai ta fada wa cikin ruwa wasu suka nutse.

“Da hannuna mun samo gawarwaki tara wasu kuma har zuwa yau ba mu samo su ba,” in ji Aliyu.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

Aliyu ya kara da cewa, “Wannan ba shi ne karon farko da yara suke mutuwa ba, ko lokacin azumi yara hudu sun mutu saboda debo wa iyayensu ruwa.”

Muhammad Lawal Yusif daya daga cikin wadanda ya rasa diyarsa budurwa ‘yar shekaru 17, wadda aka shirya aurar da ita bayan babbar Sallah, mai suna Zainab da kaninta Aliyu wanda aka tsami gawarwakinsu, ya nuna matukar damuwarsa kan faruwar lamarin.

Muhammad Lawal ya kara da cewa, “Matsalar ruwan sha ne ya sanya muke aiken yaran zuwa hayin gulbi su hau kwale-kwale Naira 10 su sayo jarka Naira 10, sai su kara hawa kwale-kwale Naira 10 a kawo su bakin gaba su fito su kawo gida a yi musu abunci da wanki da shi.”

Mahaifin yaran ya koka sosai ganin yadda a ce Hedikwatar Jihar gwamnati Jihar Zamfara ta gaza samar musu ruwan sha shekara da shekaru kuma akai-akai sai asara rayuka ake yi.

A kan haka ne Lawal ya yi kira ga sabuwar Gwamnatin da za a kaddamar nan da ‘yan kwanaki da ta dubi halin da suke ciki na rashin ruwa domin kawo karshen matsalar.

A binciken da wakilinmu ya yi, ya gano cewa matsalar na ci gaba da faruwa ne sakamakon rashin ba da isashshen kudaden tafiyar da ma’aikatar ruwan a jihar.

Sannan, matsalar wutar lantarki na daya daga cikin dalilin da ya sa ake samun matsalar ruwan.

Kan wannan matsalar, ‘yan jarida sun nemi jin ta bakin Manajan Gudanarwa na ruwa na Gusau, Buhari Dosara, ya bayyana cewa, matsalar wutar lantarki ne babbar matsalar da ke jawo rashin samun wadataccen ruwa a fadin jihar.

Sannan ya koka da da cewa, “Tun daga lokacin gwamnatin Yariman Bakura zuwa yau ma’aikatan ne kadai ke biyan kudin ruwa. Ko su ma babu wanda yake ba da sama da 1000.

“Amma su mutanen gari kyauta suke shan ruwa kuma ga jama’a na karuwa a Gusau ko da yaushe don haka wannan shi ne babban kalubalan da muke fuskanta.”

Manajan ya kara da cewa, “Ka san wata-wata da gwamnati ke ba mu da su ne mu ke maneji wajen sayen gas da kayan sarrafa ruwan don rabawa ga mutanan gari.”

A wani labari kuma, a daidai lokacin da Zamfara ke fama da matsalar ruwa, a makon jiya Hukumar tsaro ta farin kaya ta (NSCDC) ta kama mota dauke da alif wanda za a fitar da shi daga Jihar cikin dare domin kawai Jihar Katsina da Kano.

‘Yan jaridu sun sun tubi, Kwamadan hukumar NSCDC a jihar, Muhammad Mu’azu ya shaida wa manema labarai cewa an kama motar shake da alif na ruwa ne.

“Jami’anmu sun samu nasara kama wannan kaya kuma muna bincike a kai don yanzu haka mun tabbatar da cewa, an kai wasu kayan Katsina da Kano. Mun rubuta wa gwamnatin jiha.”

Ya ce suna kokarin bin sawun inda aka kai alif din domin kwato su.

“Don yanzu haka muna tsare da mai kula da dakin ajiye kayan hukumar ba da ruwan a karkara kuma da sa hannunsa ne aka fidda kayan na Jihar Zamfara domin kai su Katsina da Kano,” in ji kwamanda NSCDC”.

Kwamandan ya nemi manema labarai su ji ta bakin mai kula da dakin ajiyar ma’aikatar hukumar ruwan da ake zargin shi ne ya ba da takardun fidda kayan.

Ya shaida wa manema labarai cewa, shi aikinsa bin umarnin babban manajan ma’aikatar na ba da kaya duk sanda aka nemi ya ba da, kuma yana da shaidar takardar da shi babban manajan ma’aikatar ya sanya hannu na ya b ada kayan zuwa inda za a kai su, kamar yadda jami’an mai kula da ajiye kayan hukumar ruwa na Jihar Zamfara ya shaida da ke fuskantar tuhumar jami’an tsaro.

Kwamadan NSCDC ya tabbatar da cewa duk wanda bincike ya nuna cewa na da hannu a lamarin tabbas za su kama shi kuma za su gurfanar da shi a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GabaKogiMatsalaNutsewaRuwaRuwan ShaYaraZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Next Post

Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

Related

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

3 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

8 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

9 hours ago
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

19 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

21 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

22 hours ago
Next Post
Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.