• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Amfani Da Fasahar Zamani Ya Wajaba Matuƙar Ana So A Yi Nasara – Gwamna Dauda

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Matsalar Tsaro: Amfani Da Fasahar Zamani Ya Wajaba Matuƙar Ana So A Yi Nasara – Gwamna Dauda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada buƙatar amfani da manyan na’urorin zamani domin yaƙi da matsalar tsaro a Jihar Zamfara, Arewa da ma Nijeriya baki ɗaya.

Gwamnan Jihar Zamfara da wasu gwamnonin jihohi sun gana da Amina J. Mohammed, Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin Washington D.C. ranar Juma’a.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar ta bayyana cewa taron ya samu halartar gwamnonin jihohin Zamfara, Benuwai, Jigawa, Kaduna, Katsina, Kebbi, da Neja.

  • Nijeriya Ba Ta Shirya Samar Da ‘Yansandan Jihohi Ba – Sufeton ‘Yansanda

Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina J. Mohammed ta yaba wa Gwamnonin kan ƙoƙarin da suke yi na ganin an magance matsalolin yankin.

“Kasancewar ku a nan ya nuna ƙwaƙƙwarar sha’awar da Gwamnonin Arewa ke yi na aiwatar da sauyi a jihohinsu.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Tsaro

Da yake bayyana halin da ake ciki a Zamfara ga Mataimakiyar Babban Sakataren, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana muhimmiyar rawar da fasahar zamani za ta iya takawa wajen inganta tsaro da kuma buƙatar haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen amfani da ƙarfin fasahar da ta haɗa da yin amfani da fasahar ƙere-ƙere, na’urorin tantance kwayoyin halitta da kyamarorin sa ido (CCTV).

“Muna nan da matsalolin da dama, amma babban ƙalubalenmu shi ne rashin tsaro, kuma dole ne a yi wani abu a kai.

“Saboda rashin tsaro, noma ya gagara. Muna buƙatar taimako wajen bunƙasa noma ta yadda za mu iya amfani fasaha wajen yaƙi da wannan tada ƙayar baya. Muna fatan samun mafita ga waɗannan matsalolin yayin waɗannan tarukan. Na karɓi mulki a jiha mai cike da rashin aiki tare da ƙarancin ci gaba.

“Na ayyana dokar ta-ɓaci a fannin ilimi da lafiya. Dole ne mu ɗauki matakin gaggawa don magance waɗannan batutuwa masu muhimmanci; in ba haka ba, makomar mu za ta yi muni. Muna buƙatar tallafi mai muhimmanci don shawo kan waɗannan ƙalubalen da kuma tabbatar da kyakkyawar makoma ga jama’armu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FasahaTsaroZamaniZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakatar Da Ganduje: Alkalin Ya Yi Watsi Da Umurnin Da Ya Bayar

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga G7 Da Ta Sauya Tsohuwar Halayyar Dora Alhaki Kan Wasu

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

2 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

7 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

8 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

9 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

12 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga G7 Da Ta Sauya Tsohuwar Halayyar Dora Alhaki Kan Wasu

Sin Ta Yi Kira Ga G7 Da Ta Sauya Tsohuwar Halayyar Dora Alhaki Kan Wasu

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.