• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Kaduna Za Ta Sauya Wa Makarantu 359 Matsuguni

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Kaduna Za Ta Sauya Wa Makarantu 359 Matsuguni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana cewar gwamnatin jihar za ta sauya wa makarantu 359 da ke wuraren da ake fama da matsalar tsaro matsuguni a jihar.

A ranar 7 ga watan Maris ne, ‘yan bindiga suka yi garkuwa da dalibai sama da 250 daga makarantar firamare da ke garin Kuriga, daga bisani maharan suka sako dalibai 167 makonni biyu bayan wani hari da sojoji suka kai musu.

  • Kwastam ta Mika Jabun Dalar Amurka Da Jirage Marasa Matuka 148 Da Ta Kwace Ga EFCC Da Sojoji
  • An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar, Sani Kila ne, ya bayyana matakin yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a jihar.

Matakin, wani bangare ne na shirin gwamnatin tarayya na kare makarantu, wanda ke da nufin inganta matakan tsaro don kare cibiyoyin ilimi, dalibai da malamai daga hare-haren ‘yan bindiga.

Da yake bayyana damuwarsa kan yadda masu hannu da shuni ke kawo cikas ga harkokin tattalin arziki da zamantakewa, Gwamna Sani ya jaddada muhimmancin da ke tattare da kare fannin ilimi a jihar.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Ya nuna damuwarsa kan yadda ake samun raguwar daliban da ke shiga makarantu a jihar, inda akalla daliban Firamare sama da 200,000 suka daina zuwa makaranta a zangon karatu na shekarar 2022/2023.

Gwamna Sani ya danganta koma bayan da aka samu da rashin tsaro musamman a yankunan Chikun da Birnin Gwari da Kajuru da Giwa da kuma Igabi, inda matsalar tsaro ta fi kamari.

“Domin samar da ilimi ga yaran da ke zaune a yankunan da ake fama da matsalar tsaro, gwamnati ta fara shirin sauya wa makarantu 359 matsuguni saboda tsaro,” in ji Gwamna Sani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiKadunaMakarantuMatsalar TsaromatsuguniUba Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin: A Samar Da Karin Alfanu Da Tsaro Mai Dorewa Ga Jama’a

Next Post

Shekaru 14 Bayan Rasuwar Yar’Adua: Wasu Nasarori Da Ya Cimma A Rayuwarsa

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

10 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

13 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

21 hours ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

22 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

1 day ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanaki 10 A Faransa Da Birtaniya

1 day ago
Next Post
Shekaru 14 Bayan Rasuwar Yar’Adua: Wasu Nasarori Da Ya Cimma A Rayuwarsa

Shekaru 14 Bayan Rasuwar Yar’Adua: Wasu Nasarori Da Ya Cimma A Rayuwarsa

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.