• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

by Mairo Muhammad Mudi
4 weeks ago
in Labarai
0
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin wani lokaci da ake cike na damuwa, sakamakon yawaitar rashin aikin yi, shaye-shaye da kuma damfarar yanar gizo tsakanin matasanmu, na samu damar ganin wani labari mai dadi daga Suleja, labari na ci gaba da kwazo daga hannun matasa da ya cancanci tallafi da goyon bayan kowa da kowa.

An gayyace ni a matsayin daya daga cikin masu sharhi a wani babban taron zamani da aka kira da; “The Digital Dominance Summit”, wanda taken sa ya kasance a matsayin ‘Gina Alamar Kasuwanci Mai Riba A Sabon Tattalin Arziki: Talla, Dabara Da Kuma Tasiri A Yanar Gizo.’ Kafin na amince da zuwa, shugaban taron kuma wanda ya kafa ‘Balpulse’, wato Coach Naseer Abdullahi, ya zo har gida ya bayyana min manufofin taron cikin kwarewa.

  • Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
  • Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A gaskiya ban cika sha’awar harkokin intanet ba, koda-yake na amfana da su kwarai da gaske. Amma da ya fara bayani mataki-mataki yadda suke tafiyar da ayyukansu, sai na kasa rufe baki saboda mamaki. Gaskiya matasa suna da fasaha da basirar da za su iya jan kansu daga kuncin talauci zuwa abin alfaharin al’umma.

Wannan taro dai, ya mayar da hankali ne a kan ‘affiliate marketing’, wanda ake nufi da “Talla mai cin gajiyar sakamako”. A nan, mutum na samun riba ta hanyar tallata kaya ko hidima na wani kamfani a kafafen sada zumunta ko yanar gizo. Da zarar wani ya saya daga hanyar da aka tallata, kai ma za ka samu naka kason. Yana da sauki wajen fahimta, amma babbar ribar tana tattare da cinikin kayan duk da mai tallar bai zuba jarin ko sisi ba. Wasu matasa a fadin Nijeriya, na samun miliyoyin kudi daga wannan fanni ba tare da karya doka ba.

Da farko, ni dai na je ne da niyyar yin kashedi a kan matsalar shaye-shaye da damfarar yanar gizo da matasa ke fadawa ciki dumu-dumu. Ko da kuwa, ba su ware lokaci domin wannan batu ba, ni dai ina shirin yin magana a kansa, domin kuwa shi ne babban kalubale a al’ummarmu. Amma abin mamaki, taron sai ya zame min wata hanya ta ganin wani sabon al’amari mai ban sha’awa daga matasanmu.

Labarai Masu Nasaba

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

A can ne na hadu da wani matashi mai hazaka da kwazo, Faisal Ibrahim Abdullahi, wanda ya shaida min cewa; ya je Jihar Legas ne domin koyon fasahar ‘Epody Resin’, wato kera kayan ado da kayan daki na zamani da ake yi da sinadaran resin. Har yanzu, shi ne kadai daga yankinmu da ya mallaki wannan fasaha. Amma yana da burin koyar da sauran matasa muddin aka tallafa masa.

Na tsaya ina kallon kayan da ya nuna min na daki da ado, wanda na dauka cewa; ana yin su ne daga kasashen waje. Sai na ji cewa, “toh, dama a Suleja ake wannan?” Gaskiya wannan irin kwazo yana da bukatar tallafi, ba yabo kadai ba.

Bayan haka, taron ya kunshi gasa da horo a harkokin kasuwanci ta yanar gizo, inda matasa da dama suka samu kyaututtuka masu daraja daga ciki har da wata budurwa mai suna Blessing Paul da ta lashe kyautar mota da wasu da suka samu kyautar kudi.

Amma abin da ya dada daga min hankali shi ne, yadda galibin matasan da ke cin moriyar wannan dandali ba ’yan asalin Suleja ba ne. Wadanda suka fi mayar da hankali su ne daga wasu jihohi, suna rungumar dama da hannuwa biyu. Amma mu dai har yanzu muna ganin wadannan matasa kamar ‘yan damfara ne.

Wasu daga cikin masu rike da madafun iko ma sun yi watsi da gayyatarsu, idan ban da Mataimakin Shugaban karamar Hukumar Suleja da na Shiroro. Wasu daga cikin manyan sun yi wa su Coach Naseer mumunar fahimta, har suna yi musu kallon ‘Yahoo boys’ ne.

Ina ganin lokaci ya yi da za mu farka daga barci. Wadannan matasa suna kokari ne wajen gyara rayuwarsu ba tare da aikata laifi ba. Wajibi ne shugabanni da masu hannu da shuni da kuma masu zurfin tunani su rungumi irin wannan dandali, domin amfanin kowa da kowa.

Ga wasu daga cikin fa’idojin wannan dandalin talla na yanar gizo (affiliate marketing):

1- karfafa Matasa: Yana koya musu dogaro da kai da kuma dabarun kasuwanci.

2- Rage Aikata Laifuka: Matashin da ke da abin yi ba zai shiga yin shaye-shaye ko damfara ba.

3- Ci Gaban Al’umma: Nasarar mutum daya tana karfafa gwiwar wasu.

4- Samar Da Arziki: Wasu matasan da ke amfani da wannan dandali sun fara daukar ma’aikata, domin hannunsu ya fara maikon shuni.

5- Shiga Duniya: Matasanmu na iya fafatawa da sauran kasashen duniya daga cikin gida.

Don haka, ina kira ga Shuwagabannin Jihar Neja da na Suleja, ’yan kasuwa, manyan malamai da shugabannin gargajiya, da su bayar da goyon baya ga irin wannan yunkuri. Wannan dama ce ta fita daga kangin dogaro da gwamnati da kuma sauya tunanin cewa; dole sai an yi bariki ko kuma damfara kafin a samu kudi.

Haka zalika, kuna iya tallafa wa Faisal; domin ya koyar da matasa. Kuna kuma iya bayar da kayan aiki ko kudin horo. Amma mafi muhimmanci shi ne, ba su karfin gwiwa.

A nan ne, zan yi kira ga adali, manomin Gwamnan Jihar Neja; da ya bude wa wannan matashi kofar masana’antar Ladi Kwali, domin koyar da matasa wannan fasaha.

Yanzu duniya ta koma ta yanar gizo, wanda bai da fasahar zamani; kamar wanda bai iya karatu ba ne. Muna da zabi: mu goyi bayan irin su Coach Naseer da Faisal, ko kuma mu ci gaba da zargin su har su bar mu su tafi su samu nasara a inda ake mutunta fasaha irin tasu.

Daga Suleja nake kawo muku wannan labari mai dadi. Labarin harsashen nasara, ci gaba da inganci da ke kusa da mu, sai dai kash! Yawancinmu, ba ma ganin abin a haka.

Mu tashi tsaye. Mu goyi bayan kwazon matasanmu, kafin lokaci ya kure mana, ko wani ya zo ya amfana da su, mu kuma mu zauna muna ta faman korafi maras amfani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Next Post

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

11 hours ago
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC
Labarai

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

11 hours ago
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
Labarai

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

16 hours ago
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

17 hours ago
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC
Labarai

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

18 hours ago
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji
Labarai

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

20 hours ago
Next Post
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

July 20, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

July 20, 2025
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

July 20, 2025
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

July 20, 2025
Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

July 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

July 20, 2025
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

July 20, 2025
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

July 20, 2025
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

July 20, 2025
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.