ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Lamido

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya gargadi Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi taka tsantsan wajen yin amfani da karfin gwamnati don gurgunta jam’iyyun adawa, yana mai cewa irin wadannan ayyukan na iya kawo masa matsala a 2027.

Tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata hira ta musamman da ya yi da manema labarai a garin Birninkudu da ke karamar hukumarsa, jim kadan bayan an zabe shi a matsayin wakilin kasa don wakiltar karamar hukumar Birninkudu a babban taron jam’iyyar PDP mai zuwa.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Gabon
  • Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta

Alhaji Sule Lamido ya nuna damuwarsa kan yadda ake zargin jam’iyyar APC da Shugaba Tinubu ke amfani da cibiyoyin gwamnati wajen yin barazana, cin zarafi, da kuma raunana jam’iyyun adawa a shirye-shiryen tsayawa takara a wa’adi na biyu a 2027. Ya bayyana wadannan ayyukan a matsayin illa ga shugaban kasa da tsarin siyasa.

ADVERTISEMENT

A matsayinsa na daya daga cikin iyayen da suka kafa jam’iyyar PDP kuma mamba a kwamitin amintattu, Lamido ya ce, “Idan ka kalli yadda mutane ke ficewa daga PDP, abin takaici ne kuma barazana ce ga kasar nan.

“Kasar da dimokuradiyya ke cikin babban hadari saboda tarwatsa ‘yan adawa ta amfani da cibiyoyin gwamnati kamar INEC, ‘yansanda, DSS, da EFCC, ba wai kawai kuna tarwatsa ‘yan adawarku ba har ma da kanku.”

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Ya kara da cewa, “An gina tushen dimokuradiyya a kan ‘yanci, da adawa. Tinubu, a cikin hikimarsa, ya yi imanin cewa ta hanyar lalata jam’iyyun adawa kamar PDP, yana bunkasa arzikinsa na siyasa. “Abin takaici, yana da wayo dan kadan, saboda tarwatsa PDP a matsayin jam’iyyar siyasa yana nufin za a lalata Nijeriya da kanta, kuma komai zai ruguje a kansa.”

Lamido ya bayyana kwarin gwiwar cewa wadanda suka bar PDP za su dawo. “Kawai jira watanni biyar ko shida, kuma a karshen wannan shekarar, za ku gani. Tinubu ya kashe kansa a siyasa. Wadanda ke tare da shi ma suna kashe kansu a siyasa.

Ya kara da cewa, “Jam’iyyar siyasa ko ta yaya ya kamata ta iya kare kanta daga ‘yan adawa. Idan APC tana aiki, wannan ba matsala ba ce. Amma lokacin da gwamnati da shugaban kasa ke yaki da PDP, wannan yana da hadari. PDP a matsayinta na jam’iyyar adawa za ta iya yaki da jam’iyyar APC mai mulki, kuma APC za ta iya yaki da mu. Amma idan duk gwamnatin tarayya ta yi amfani da kayan aikinta don yaki da mu, wannan shi ne ainihin hadari. ”

Lamido ya ci gaba da cewa, “Ba APC ce ke yaki da mu ba, gwamnati ce ke yaki da mu. Tinubu ne a matsayinsa na shugaban kasa yake yaki da mu. Idan ya lalata tsarin, kawai yana gayyatar kashe kansa a siyasa. Wadanda ke biye da shi suna tsoron EFCC. Amma me ya sa ake jin tsoron EFCC? Idan kun tuna abin da Ribadu ya fada game da Shugaba Tinubu shekaru da suka wuce, me ya sa zan ji tsoronsa? “Saboda EFCC ta fallasa shi a baya, ta yaya zan ji tsoronsa?”

Ya nuna godiya da farin cikinsa game da aikin da jam’iyyar da mambobinta suka yi saboda girmama shi da ba shi mukami.

Alhaji Lamido ya kuma yaba wa PDP da kwamitin zaben bisa kyakkyawan aikin da suka yi, tare da gode wa mambobin da suka gudanar cikin tsari.

Lamido
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Lamido
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

Sashen Yawon Shakatawa Na Teku A Kasar Sin Ya Samu Gagarumin Ci Gaba A Rubu’in Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.