• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

‘Yan Nijeriya sun fara azumin wata Ramadana a bana cikin matsanancin rashin wutar lantarki a daidai lokacin da ake fuskantar matukar zafi a kasar.

Da ma dai kasar ta dade tana fama da matsalar wadatacciyar wutar lantarki, sai dai bayanan sun nuna cewa a wannan lokaci rashin wutar lantarkin ya yi matukar karuwa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

A wannan karon dai, gwamnatin Nijeriya ta dora alhakkin karancin wutar lantarkin kan rashin isasshiyar iskar gas. Abin da ya sa ko a watan jiya ma’aikatar wutar lantarkin tare da hadin gwiwar ma’aikatar albarkatun man fetur na kasar nan suka kafa wani kwamiti domin ya lalubo hanyar magance karancin gas da kamfanonin samar da wutar lantarki ke fama da shi.

Sannan a daya bangaren kuma, akwai matsalar lalata manyan turakun wutar lantarki wanda ake zargin wasu bata-gari suna yi. Na baya-bayan nan shi ne na lalacewar babban layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Katampe kamar yadda babbar jami’ar hulda da jama’a ta kamfanin rarraba wutar lantarki (TCN), Ndidi Mbah ta bayyana.

Misis Mbah ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya cewa, wannan ne karon na biyar da ake samun irin wannan matsalar ta katsewar babban layin wutar lantarki tsakanin watan Fabrairu zuwa Maris.

Sai dai shugaban kamfanin SkyMark Energy and Power Ltd, Muhammad Sale Hassan, sannan ya kasance mai sharhi kan harkokin makamashi yana ganin cewa wannan laifin na kamfanoni masu zaman kansu ne (Discos), wadanda suke rarraba wutar lantarki.

Ya ce kamfanonin ba su da kwarewa da isasshen karfin jari da za su iya ci gaba da gudanar da aikin rarraba wutar lantarki. Sai dai kamfanonin sun sha musanta irin wadannan zargi da ake musu.

Mai sharhin ya ce suna samun matsala ne a bargaren rarraba wutar lantarki, amma ba a bangaren samar da ita ba.

Ko a makon jiya ma, ministan wutar lantarki na Nijeriya, Bayo Adelabu ya yi barazanar kwace lasisin kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasar nan, saboda yawan dauke-dauken wutan da ake yi. Yana mai cewa ba za a lamunci yanayin da suke saka mutane na karancin wutar lantarki ba a fadin kasar nan.

Sai dai masana na ganin cewa dole ne gwamnatin Nijeriya ta shafa wa fuskarta toka idan tana so ta kawo karshen matsalar wutar lantarki, domin kuwa da wahala muradinta na samar da ci gaba a kasar ya cika muddin ba a samar da isasshen hasken wutar lantarki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

Next Post

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

38 minutes ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

4 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

12 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

13 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

14 hours ago
Next Post
Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al'ummar Nafada A Jihar Gombe

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.