• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

‘Yan Nijeriya sun fara azumin wata Ramadana a bana cikin matsanancin rashin wutar lantarki a daidai lokacin da ake fuskantar matukar zafi a kasar.

Da ma dai kasar ta dade tana fama da matsalar wadatacciyar wutar lantarki, sai dai bayanan sun nuna cewa a wannan lokaci rashin wutar lantarkin ya yi matukar karuwa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

A wannan karon dai, gwamnatin Nijeriya ta dora alhakkin karancin wutar lantarkin kan rashin isasshiyar iskar gas. Abin da ya sa ko a watan jiya ma’aikatar wutar lantarkin tare da hadin gwiwar ma’aikatar albarkatun man fetur na kasar nan suka kafa wani kwamiti domin ya lalubo hanyar magance karancin gas da kamfanonin samar da wutar lantarki ke fama da shi.

Sannan a daya bangaren kuma, akwai matsalar lalata manyan turakun wutar lantarki wanda ake zargin wasu bata-gari suna yi. Na baya-bayan nan shi ne na lalacewar babban layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Katampe kamar yadda babbar jami’ar hulda da jama’a ta kamfanin rarraba wutar lantarki (TCN), Ndidi Mbah ta bayyana.

Misis Mbah ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya cewa, wannan ne karon na biyar da ake samun irin wannan matsalar ta katsewar babban layin wutar lantarki tsakanin watan Fabrairu zuwa Maris.

Sai dai shugaban kamfanin SkyMark Energy and Power Ltd, Muhammad Sale Hassan, sannan ya kasance mai sharhi kan harkokin makamashi yana ganin cewa wannan laifin na kamfanoni masu zaman kansu ne (Discos), wadanda suke rarraba wutar lantarki.

Ya ce kamfanonin ba su da kwarewa da isasshen karfin jari da za su iya ci gaba da gudanar da aikin rarraba wutar lantarki. Sai dai kamfanonin sun sha musanta irin wadannan zargi da ake musu.

Mai sharhin ya ce suna samun matsala ne a bargaren rarraba wutar lantarki, amma ba a bangaren samar da ita ba.

Ko a makon jiya ma, ministan wutar lantarki na Nijeriya, Bayo Adelabu ya yi barazanar kwace lasisin kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasar nan, saboda yawan dauke-dauken wutan da ake yi. Yana mai cewa ba za a lamunci yanayin da suke saka mutane na karancin wutar lantarki ba a fadin kasar nan.

Sai dai masana na ganin cewa dole ne gwamnatin Nijeriya ta shafa wa fuskarta toka idan tana so ta kawo karshen matsalar wutar lantarki, domin kuwa da wahala muradinta na samar da ci gaba a kasar ya cika muddin ba a samar da isasshen hasken wutar lantarki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

Next Post

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Related

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

15 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

44 minutes ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

1 hour ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

5 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

17 hours ago
Next Post
Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al'ummar Nafada A Jihar Gombe

LABARAI MASU NASABA

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.