• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

‘Yan Nijeriya sun fara azumin wata Ramadana a bana cikin matsanancin rashin wutar lantarki a daidai lokacin da ake fuskantar matukar zafi a kasar.

Da ma dai kasar ta dade tana fama da matsalar wadatacciyar wutar lantarki, sai dai bayanan sun nuna cewa a wannan lokaci rashin wutar lantarkin ya yi matukar karuwa.

  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya
  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

A wannan karon dai, gwamnatin Nijeriya ta dora alhakkin karancin wutar lantarkin kan rashin isasshiyar iskar gas. Abin da ya sa ko a watan jiya ma’aikatar wutar lantarkin tare da hadin gwiwar ma’aikatar albarkatun man fetur na kasar nan suka kafa wani kwamiti domin ya lalubo hanyar magance karancin gas da kamfanonin samar da wutar lantarki ke fama da shi.

Sannan a daya bangaren kuma, akwai matsalar lalata manyan turakun wutar lantarki wanda ake zargin wasu bata-gari suna yi. Na baya-bayan nan shi ne na lalacewar babban layin wutar lantarki na Shiroro zuwa Katampe kamar yadda babbar jami’ar hulda da jama’a ta kamfanin rarraba wutar lantarki (TCN), Ndidi Mbah ta bayyana.

Misis Mbah ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya cewa, wannan ne karon na biyar da ake samun irin wannan matsalar ta katsewar babban layin wutar lantarki tsakanin watan Fabrairu zuwa Maris.

Sai dai shugaban kamfanin SkyMark Energy and Power Ltd, Muhammad Sale Hassan, sannan ya kasance mai sharhi kan harkokin makamashi yana ganin cewa wannan laifin na kamfanoni masu zaman kansu ne (Discos), wadanda suke rarraba wutar lantarki.

Ya ce kamfanonin ba su da kwarewa da isasshen karfin jari da za su iya ci gaba da gudanar da aikin rarraba wutar lantarki. Sai dai kamfanonin sun sha musanta irin wadannan zargi da ake musu.

Mai sharhin ya ce suna samun matsala ne a bargaren rarraba wutar lantarki, amma ba a bangaren samar da ita ba.

Ko a makon jiya ma, ministan wutar lantarki na Nijeriya, Bayo Adelabu ya yi barazanar kwace lasisin kamfanonin rarraba wutar lantarki na kasar nan, saboda yawan dauke-dauken wutan da ake yi. Yana mai cewa ba za a lamunci yanayin da suke saka mutane na karancin wutar lantarki ba a fadin kasar nan.

Sai dai masana na ganin cewa dole ne gwamnatin Nijeriya ta shafa wa fuskarta toka idan tana so ta kawo karshen matsalar wutar lantarki, domin kuwa da wahala muradinta na samar da ci gaba a kasar ya cika muddin ba a samar da isasshen hasken wutar lantarki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

Next Post

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

6 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

8 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

9 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

11 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

11 hours ago
Next Post
Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al'ummar Nafada A Jihar Gombe

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.