• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayakan FPL 9 Sun Mika Wuya Ga Gwamnatin Sojin Nijar

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mambobin kungiyar ‘yan tawaye tara dake neman a sako hambararren shugaban kasar Nijar sun mika wuya, kamar yadda jami’an kasar da sojoji ke mulka suka bayyana.

 

An kafa kungiyar ‘yan tawayen Patriotic Liberation Front (FPL) a watan Agustan shekarar 2023, wata guda bayan hambarar da zababben shugaban Jamhuriyar Nijar Mohamed Bazoum a wani juyin mulki da sojoji suka yi.

  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: PDP Ta Lashe Dukkanin Kujerun Shugabanni A Zamfara
  • Manomanmu Sun Tabka Asarar Sama Da Naira Miliyan 100 A Harin ‘Yan Bindiga – Dan Majalisa

Tun a wancan lokaci Bazoum na tsare da matarsa Hadiza a fadar shugaban kasa da ke Yamai babban birnin kasar.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Gwamnan Agadez, wani jami’in yankin hamadar Arewacin kasar dake kusa da kasar Libya ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa, mayakan FPL tara sun tuba tare da mika makamansu da alburusai a yayin wani biki a gaban Janar Ibra Boulama.

 

Mambobin FPL sun fara mika wuya ne a farkon wannan wata bayan tattaunawa mai ma’ana da wasu masu fada aji na kasar, kamar yadda kafar yada labarai ta Air-Info ta ruwaito.

 

A ranar 1 ga watan Nuwamba mai magana da yawun FPL Idrissa Madaki tare da wasu mambobi uku sun mika kansu a lokuta daban-daban a wasu garuruwa biyu da ke kusa da kan iyakar kasar Libya, kamar yadda sojojin Nijar da gidan talabijin na kasar suka bayyana.

 

A makon da ya gabata, an cire wa shugaban FPL Mahmoud Sallah, da kuma wasu mutane bakwai na gwamnatin Bazoum da ake zargi da kai hare-haren ta’addanci. ‘yancin zama ‘yan kasa na dan lokaci.

 

Sallah ya dauki alhakin kai hare-hare kan sojoji a Arewa da kuma lalata wani muhimmin bututun mai da ke dauke da danyen mai zuwa Benin a watan Yuni. Ya kuma yi barazanar kai hari a wurare masu mahimmanci.

 

Wata kungiyar ‘yan tawayen da ita ma ta ke neman a sako Bazoum, da ake kira, “Patriotic Front for Justice” (FPJ), tana tsare babban jami’in hukumar soji ta yankin Arewa maso Gabashin Bilma da wasu jami’an tsaronsa hudu, wadanda aka yi garkuwa da su bayan wani kwanton bauna a tun watan Yunin da ya gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

6 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

6 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

7 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

8 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

10 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

11 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ma'aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.