ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manomanmu Sun Tabka Asarar Sama Da Naira Miliyan 100 A Harin ‘Yan Bindiga – Dan Majalisa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Majalisa

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Birnin Gwari, Hon. Bashir Zubairu Birnin Gwari (Chiroma), ya ce manoma sun yi asarar sama da naira miliyan 100, sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a gonakin masara a karamar hukumar.

 

Dan majalisar ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da gidan rediyon BBC Hausa a ranar Laraba kan harin da ‘yan bindiga suka kai gonakin masara da ke Kwaga da Unguwar Zoko a karamar hukumar Birnin Gwari a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

Ya ce idan har gwamnati ta gaza magance irin wannan ta’asa, to jama’a ba su da wani zabi illa su kare kansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Asara ce babba ta sama da naira miliyan 100, kuma su ’yan bindiga ba za su daina ba, domin wani abu ne da suka yi watanni biyu zuwa uku da suka wuce. Suna ikirarin cewa an kai wa mutanensu hari, an lalata musu dukiyoyi, kuma dole ne a mayar musu da makamansu da aka kwace,” in ji shi.

 

Rahotanni sun bayyana cewa harin da aka kai a gonar masara a ranar Lahadin da ta gabata ya faru ne kasa da sa’o’i 48 bayan shugabannin addini da na al’umma sun gana da shugabannin ‘yan bindiga a yankin, inda suka tattauna batun zaman lafiya.

 

Dangane da yarjejeniyar zaman lafiya da ake cimma, dan majalisar ya ce mutanen kauyukan da abin ya shafa da suka yi asarar dukiyoyinsu da ‘yan uwa a sakamakon hare-haren ya kamata a biya su diyya kan asarar da suka yi.

 

“Ba zai yiwu a zauna da ’yan bindiga a cikin yarjejeniyar zaman lafiya ba, daga baya a ba su makudan kudade, baya ga dukiyar da suka kwace daga hannun mutanen kauyukan da ba su ji ba ba su gani ba, mutanen da suka kashe, da dukiyoyin da suka lalata. Ka yi tunanin irin mummunar asarar da aka yi wa manoma, amma duk da haka kuna son a samu yarjejeniyar zaman lafiya da su.

 

“A kan wannan yarjejeniyar zaman lafiya, ina so in yi kira ga shugabanni daga gwamnatin tarayya da su sani cewa wani bangare na yarjejeniyar ya kamata ya hada da biyan diyya ga mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da aka lalatar da kayayyakin gonakinsu,” in ji shi.

 

Chiroma ya kara da cewa, a baya, a wata yarjejeniyar zaman lafiya, an gayyaci wasu shugabannin ‘yan bindiga zuwa fadar Sarkin Birnin Gwari, kuma an ba su makudan kudade a cikin yarjejeniyar zaman lafiya.

 

“A halin da ake ciki, talakawan da aka sace iyalansu da aka lalatar da rayuwarsu ba su samu komai ba,” in ji shi.

 

Ya bayyana cewa duk da ba wa fararen hula makamai ba shi ne mafita ba, amma idan lamarin ya ta’azzara, mazauna yankin za su yi wa kansu mafita.

 

Ya kuma koka da yadda ake damke mutanensa masu sayan makamai domin kare kansu, inda ya ba da misali da wasu mazauna Kutemeshi da aka kama aka tsare su a ofishin ‘yansanda a watan jiya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
kotu

Ma'aikatar Shari'a Ta Jigawa Ta Nada Alkalan Kotun Shari’a 19 Tare Da Karin Girma Ga Ma’aikata 157

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.