ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manomanmu Sun Tabka Asarar Sama Da Naira Miliyan 100 A Harin ‘Yan Bindiga – Dan Majalisa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Majalisa

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Birnin Gwari, Hon. Bashir Zubairu Birnin Gwari (Chiroma), ya ce manoma sun yi asarar sama da naira miliyan 100, sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a gonakin masara a karamar hukumar.

 

Dan majalisar ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da gidan rediyon BBC Hausa a ranar Laraba kan harin da ‘yan bindiga suka kai gonakin masara da ke Kwaga da Unguwar Zoko a karamar hukumar Birnin Gwari a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

Ya ce idan har gwamnati ta gaza magance irin wannan ta’asa, to jama’a ba su da wani zabi illa su kare kansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Asara ce babba ta sama da naira miliyan 100, kuma su ’yan bindiga ba za su daina ba, domin wani abu ne da suka yi watanni biyu zuwa uku da suka wuce. Suna ikirarin cewa an kai wa mutanensu hari, an lalata musu dukiyoyi, kuma dole ne a mayar musu da makamansu da aka kwace,” in ji shi.

 

Rahotanni sun bayyana cewa harin da aka kai a gonar masara a ranar Lahadin da ta gabata ya faru ne kasa da sa’o’i 48 bayan shugabannin addini da na al’umma sun gana da shugabannin ‘yan bindiga a yankin, inda suka tattauna batun zaman lafiya.

 

Dangane da yarjejeniyar zaman lafiya da ake cimma, dan majalisar ya ce mutanen kauyukan da abin ya shafa da suka yi asarar dukiyoyinsu da ‘yan uwa a sakamakon hare-haren ya kamata a biya su diyya kan asarar da suka yi.

 

“Ba zai yiwu a zauna da ’yan bindiga a cikin yarjejeniyar zaman lafiya ba, daga baya a ba su makudan kudade, baya ga dukiyar da suka kwace daga hannun mutanen kauyukan da ba su ji ba ba su gani ba, mutanen da suka kashe, da dukiyoyin da suka lalata. Ka yi tunanin irin mummunar asarar da aka yi wa manoma, amma duk da haka kuna son a samu yarjejeniyar zaman lafiya da su.

 

“A kan wannan yarjejeniyar zaman lafiya, ina so in yi kira ga shugabanni daga gwamnatin tarayya da su sani cewa wani bangare na yarjejeniyar ya kamata ya hada da biyan diyya ga mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da aka lalatar da kayayyakin gonakinsu,” in ji shi.

 

Chiroma ya kara da cewa, a baya, a wata yarjejeniyar zaman lafiya, an gayyaci wasu shugabannin ‘yan bindiga zuwa fadar Sarkin Birnin Gwari, kuma an ba su makudan kudade a cikin yarjejeniyar zaman lafiya.

 

“A halin da ake ciki, talakawan da aka sace iyalansu da aka lalatar da rayuwarsu ba su samu komai ba,” in ji shi.

 

Ya bayyana cewa duk da ba wa fararen hula makamai ba shi ne mafita ba, amma idan lamarin ya ta’azzara, mazauna yankin za su yi wa kansu mafita.

 

Ya kuma koka da yadda ake damke mutanensa masu sayan makamai domin kare kansu, inda ya ba da misali da wasu mazauna Kutemeshi da aka kama aka tsare su a ofishin ‘yansanda a watan jiya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
kotu

Ma'aikatar Shari'a Ta Jigawa Ta Nada Alkalan Kotun Shari’a 19 Tare Da Karin Girma Ga Ma’aikata 157

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.