ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manomanmu Sun Tabka Asarar Sama Da Naira Miliyan 100 A Harin ‘Yan Bindiga – Dan Majalisa

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Majalisa

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Birnin Gwari, Hon. Bashir Zubairu Birnin Gwari (Chiroma), ya ce manoma sun yi asarar sama da naira miliyan 100, sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a gonakin masara a karamar hukumar.

 

Dan majalisar ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da gidan rediyon BBC Hausa a ranar Laraba kan harin da ‘yan bindiga suka kai gonakin masara da ke Kwaga da Unguwar Zoko a karamar hukumar Birnin Gwari a ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad

Ya ce idan har gwamnati ta gaza magance irin wannan ta’asa, to jama’a ba su da wani zabi illa su kare kansu.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Asara ce babba ta sama da naira miliyan 100, kuma su ’yan bindiga ba za su daina ba, domin wani abu ne da suka yi watanni biyu zuwa uku da suka wuce. Suna ikirarin cewa an kai wa mutanensu hari, an lalata musu dukiyoyi, kuma dole ne a mayar musu da makamansu da aka kwace,” in ji shi.

 

Rahotanni sun bayyana cewa harin da aka kai a gonar masara a ranar Lahadin da ta gabata ya faru ne kasa da sa’o’i 48 bayan shugabannin addini da na al’umma sun gana da shugabannin ‘yan bindiga a yankin, inda suka tattauna batun zaman lafiya.

 

Dangane da yarjejeniyar zaman lafiya da ake cimma, dan majalisar ya ce mutanen kauyukan da abin ya shafa da suka yi asarar dukiyoyinsu da ‘yan uwa a sakamakon hare-haren ya kamata a biya su diyya kan asarar da suka yi.

 

“Ba zai yiwu a zauna da ’yan bindiga a cikin yarjejeniyar zaman lafiya ba, daga baya a ba su makudan kudade, baya ga dukiyar da suka kwace daga hannun mutanen kauyukan da ba su ji ba ba su gani ba, mutanen da suka kashe, da dukiyoyin da suka lalata. Ka yi tunanin irin mummunar asarar da aka yi wa manoma, amma duk da haka kuna son a samu yarjejeniyar zaman lafiya da su.

 

“A kan wannan yarjejeniyar zaman lafiya, ina so in yi kira ga shugabanni daga gwamnatin tarayya da su sani cewa wani bangare na yarjejeniyar ya kamata ya hada da biyan diyya ga mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da aka lalatar da kayayyakin gonakinsu,” in ji shi.

 

Chiroma ya kara da cewa, a baya, a wata yarjejeniyar zaman lafiya, an gayyaci wasu shugabannin ‘yan bindiga zuwa fadar Sarkin Birnin Gwari, kuma an ba su makudan kudade a cikin yarjejeniyar zaman lafiya.

 

“A halin da ake ciki, talakawan da aka sace iyalansu da aka lalatar da rayuwarsu ba su samu komai ba,” in ji shi.

 

Ya bayyana cewa duk da ba wa fararen hula makamai ba shi ne mafita ba, amma idan lamarin ya ta’azzara, mazauna yankin za su yi wa kansu mafita.

 

Ya kuma koka da yadda ake damke mutanensa masu sayan makamai domin kare kansu, inda ya ba da misali da wasu mazauna Kutemeshi da aka kama aka tsare su a ofishin ‘yansanda a watan jiya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
kotu

Ma'aikatar Shari'a Ta Jigawa Ta Nada Alkalan Kotun Shari’a 19 Tare Da Karin Girma Ga Ma’aikata 157

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.