• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

by Rabi'u Ali Indabawa
17 hours ago
in Labarai
0
Zaman lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Laraba ne aka gudanar da bikin Tunawa da Ranar Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya a ofishin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na Nijeriya. Babban bako a taron, Babban Hafsan Hafsoshin Tsaron Nijeriya Janar Christoper OFR. Inda a jawabinsa bayan maraba da baki ya ce, “Tunawa da Ranar Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta MDD Ta 2025, taro ne na tunatar da sadaukarwar da jarumanmu maza da mata suka yi wajen sadaukar da rayuwarsu don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.”

Ana aikin ne domin babu wata al’umma da za ta iya jure fuskantar tashe-tashen hankula a duniya, rikicin jin kai da karuwar rashin tsaro. Don haka dole ne mu ci gaba da yin aiki tare da yin magana da murya daya don samar da zaman lafiya, adalci da mutunci ga kowa. Dangane da haka, Rundunar Sojin Nijeriya ta ci gaba da dagewa wajen bin ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yana da kyau a lura cewa a matsayinta na mamba a Majalisar Dinkin Duniya, Nijeriya tun bayan samun ‘yancin ke ta ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen bayar da gudummawarta wajen wanzar da zaman lafiya da magance rikice-rikice a duniya. Bisa ga haka, sojojinmu sun yi aiki a karkashin tutar Majalisar Dinkin Duniya tare da girmamawa da ban mamaki a yankuna da dama na warware rikici a duniya.

Hakika, Nijeriya na daya daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba wajen bayar da gudunmowa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya kuma jigo a kwamitin wanzar da zaman lafiya.

Wannan ba wai yana nuna karfin sojojinmu na fuskantar barazanar da ke tasowa bane kawai, har ma da nuna imaninmu cewa zaman lafiya a duniya nauyi ne na dukkan kasashe da masu ruwa da tsaki.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Shima a nasa jawabin Janar Martin Luther Agwai cewa ya yi, “Aikin wanzar da zaman lafiya na daya daga cikin muhimman aikin Majalisar Dinkin Duniya da ake iya gani, inda sama da sojoji 87,000 ke sanye da rigar wanzar da zaman lafiya da farar hula suka taka rawa a cikin wasu ayyuka 12, daga Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo zuwa Lebanon, daga Sudan zuwa Mali. Nijeriya kuma na wakiltar ayyuka guda 8.”

Wadannan jajirtattun maza da mata suna taimakawa wajen daidaita yankuna, ba wa fararen hula kariya, tallafawa tsagaita wuta, da sake gina da amana inda ta lalace.

Mahimmanci lamari shi ne, tun lokacin da aka kafa tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta farko a shekara ta 1948, dakarun wanzar da zaman lafiya sun ceto mutum sama da miliyan biyu daga kasashe sama da 125 cikin ayyuka 71 da suka gudanar.

Tun da fari a jawabinsa na maraba, Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Kuma Mai Kula Da Ayyukan Jin Kai a Nijeriya Mohammed Malick Fall, maraba da zuwan bikin cika shekaru 77 na ayyukan samar da zaman lafiya na MDD ya yi, inda ya ce “Taro ne mai muhimmanci kuma ya zo daidai da cika shekaru 80 da kafuwar Majalisar Dinkin Duniya,” in ji shi.

“A tsawon tarihinta, Majalisar Dinkin Duniya babban aikinta ga al’ummar duniya shi ne inganta zaman lafiya, tsaro, ci gaba, da mutunta bil’adama, kuma ta yi fice a wajen cimma wadannan manufofi.”

“Tun daga 1948, Majalisar Dinkin Duniya ta sa ido kan ayyukan wanzar da zaman lafiya fiye da 70, da ceton rayuka da dama da kuma yin aiki a matsayin mai magance manyan tashe-tashen hankula.

A halin yanzu, sama da dakaru 87,000 masu sanye da kaki ana tura su cikin ayyuka mabanbanta kamar 12 a duniya.

Wanzar da zaman lafiya ya kasance daya daga cikin abubuwan da Majalisar Dinkin Duniya ta fi gani da inganci.”

“Karni na 21 ya zo da qalubalen tsaro da ba a tava ganin irinsa ba kuma masu alaqa da juna. Wadannan suna bukatar sabbin hanyoyi, kakkarfan hadin gwiwa na yanki da na duniya, da kuma sake nazarin yadda muke gudanar da ayyukan zaman lafiya-musamman yayin da rarrabuwar kawuna na siyasa ke kara hana shawo kan lamarin.

Wannan shi ne dalilin da ya sa muka sanya wa taron ranar dakarun wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a yau, taken “Makomar wanzar da zaman lafiya,” kuma ya dace sosai, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

Next Post

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

9 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

11 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

15 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

18 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Fara Biyan Tsoffin Kansiloli Na APC Sama Da Naira Biliyan 16

20 hours ago
Next Post
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.