• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ci gaba da gudanar da taron ganawa tsakanin shugabannin kasashe mambobin BRICS a birnin Kazan na kasar Rasha yanzu. A nata bangare, kasar Najeriya ta bayyana niyyarta ta shiga cikin tsarin BRICS har sau da dama. Na tuna a taron FOCAC da ya gudana a Beijing na Sin a watan Satumba da ya gabata, Yusuf Tuggar, ministan harkokin wajen kasar Najeriya ya ce, “Ba wanda zai iya hana Najeriya shiga cikin tsarin BRICS, ganin yadda kasar ta girma, kuma ta iya yanke shawara da ita kanta kan wane ne za ta yi hadin gwiwa.” 

 

Sai dai me tsarin BRICS zai haifarwa Najeriya, idan ta shiga cikin tsarin? Za mu iya samun amsa dangane da tambayar, cikin jawabin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi a taron kolin BRICS na wannan karo.

  • Sojoji Sun Ceto Mata 3, Sun Kwato Makamai A Katsina Da Zamfara
  • Tsarin BRICS Na Samun Karin Karbuwar Kasashe Daban-Daban

Jawabin shugaba Xi ya nuna alkiblar da tsarin BRICS ya dosa, da matsaya daya da mahalarta taron BRICS na wannan karo suka cimma, wanda ya kunshi wasu kalmomi masu muhimmanci, wato su: zaman lafiya, da ci gaba, da hadin gwiwa, da adalci, da kirkiro sabbin fasahohi, da kare muhalli, gami da cudanyar al’adu.

 

Labarai Masu Nasaba

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Da farko dai, yadda aka jaddada muhimmancin zaman lafiya, ya nuna cewa, kasashe mambobin BRICS sun fi son tattaunawa maimakon fada. Saboda haka, idan kasar Najeriya ta samu damar shiga cikin tsarin BRICS, to, ba ya nufi ta dauki wani bangare don takara ko fada da wasu. Maimakon haka, za ta samu karin damammakin hadin kai don tabbatar da tsaronta, da na yankin da take ciki.

 

Na biyu shi ne, batun ci gaban tattalin arziki. Ta yaya tsarin BRICS zai iya taimakawa kasashe masu tasowa wajen samun ci gaba mai dorewa? Cikin jawabinsa, shugaba Xi ya bayyana ayyukan da kasar Sin ta yi a wannan fanni, misali kafa cibiyar raya fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam ta AI, ta Sin da BRICS, da habaka hadin gwiwar da take yi tare da sauran mambobin BRICS ta fuskar masana’antu mai nasaba da fasahohin kare muhalli, da dai sauransu. Saboda haka, idan Najeriya ta shiga cikin tsarin hadin kai na BRICS, to, za ta samu damar raya wadannan bangarori, tare da inganta tsarin masana’antu a cikin gida.

 

Bangare na uku ya shafi hadin gwiwar kasashe mambobin BRICS, wadda ta kasance karkashin tsarin hadin kai na daukacin kasashe masu tasowa. Ta hanyar hada karfin wadannan kasashe, za a iya daidaita tsarin kula da al’amuran kasa da kasa, don ya zama mai adalci.

 

Hakika kasashe mambobin BRICS suna da karfin tattalin arziki. Yanzu yawan GDP nasu ya kai kashi 36% na GDPn daukacin duniya, yayin da GDPn rukunin G7 da wasu manyan kasashe dake yammacin duniya, irinsu Amurka, da Birtaniya, da Faransa, da Jamus, suka kafa, bai wuce kashi 30% na adadin duniya ba. Sa’an nan idan an binciki bangaren karuwar tattalin arziki, za a ga karuwar GDPn kasashen BRICS za ta kai kashi 4% a bana, da ta fi kashi 1.7% ta rukunin G7.

 

Yanzu haka, bisa karfinsu na fannin tattalin arziki, kasashe mambobin BRICS na kokarin samar da damammaki ga kasashe masu tasowa, don su fitar da kansu daga kangin da kasashen yamma suka saka su, da niyyar kare ikonsu na yin babakere a duniya. Saboda haka, shugaba Xi ya jaddada a cikin jawabinsa bukatar baiwa kasashe masu tasowa karin wakilci a hukumomin kasa da kasa, da damar tofa albarkacin bakinsu kan al’amuran duniya, gami da daidaita tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa.

 

A nata bangare, kasar Najeriya ta sha wahalhalu sakamakon sauyawar darajar dalar Amurka, inda take bukatar gyare-gyare kan tsarin hada-hadar kudi na duniya. A sa’i daya kuma, kasar, bisa matsayinta na babbar kasa mai dimbin al’umma da karfin tattalin arziki a Afirka, na neman damar zama mai fada a ji a hukumomin kasa da kasa daban daban. Ta haka za mu iya ganin cewa bukatun kasar Najeriya da burin tsarin BRICS daya ne.

 

Sa’an nan a bangare na karshe, wanda shi ma yana da matukar muhimmanci, za mu ambaci cudanya a fannin al’adu. A cewar shugaba Xi na kasar Sin, ya kamata a tabbatar da kasancewar mabambantan al’adu a duniyarmu, da hakuri da juna, da koyi da juna a tsakaninsu. Ta haka ake neman daidaita tsarin da kasashen yamma suka kafa na nuna girman kai a fannin tunani da na al’adu, don baiwa kasashe daban daban damar samun ‘yancin tunani, da neman hanyar raya kai da ta dace da al’adunsu. A Najeriya, al’adun kasashen yamma da tsarinsu na mulki, da ‘yan mulkin mallaka suka kawo wa kasar, sun haifar da cikas ga yanayin samun ci gaban al’adun kai a kasar, tare da haddasa dimbin matsalolin dake damun kasar har zuwa yanzu. Don neman daidaita matsalolin daga asali, da samun dabarar raya kai da ta dace da al’adun kanta, Najeriya za ta iya aiwatar da karin cudanya tare da kasashe mambobin BRICS.

 

Idan mun takaita bayanin dake sama, za mu san cewa, shiga cikin tsarin BRICS na nufin tsaro, da ci gaban tattalin arziki, da yin tasiri a fannin al’amuran kasa da kasa, da samun ‘yancin tunani, ga kasar Najeriya. Wannan nau’in alfanu shi ma ya sa tsarin BRICS ke janyo hankalin dimbin kasashe masu tasowa a kai a kai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Next Post

Xi Ya Halarci Taron Tattaunawa Na Jagororin “BRICS+” Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Related

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

3 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

7 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Halarci Taron Tattaunawa Na Jagororin “BRICS+” Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi

Xi Ya Halarci Taron Tattaunawa Na Jagororin "BRICS+" Tare Da Gabatar Da Muhimmin Jawabi

LABARAI MASU NASABA

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.