ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

by Sulaiman
11 months ago
Tarihi

Dan Adam halitta ce mai saurin mantuwa. Duk da haka, akwai wasu abubuwa da ya kamata a tuna da su.

 

Abokai, ko kun san cewa, sama da shekaru 80 da suka gabata, ‘yan Najeriya da Sinawa sun taba yaki da sojojin Japan a Burma, inda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen cin nasarar yakin da aka yi da ‘yan mulkin danniya, wato ‘yan Fascist a duniya?

ADVERTISEMENT
  • APC Ta Nemi A Soke Zaɓen Cike Gurbi A Kano Saboda Rikici
  • Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

A farkon shekarar 1944, Birtaniya ta tura wasu sojoji da aka dauka daga Najeriya, da Gold Coast (Ghana a yanzu) da sauran wurare, zuwa yankin kan iyakar Indiya da Burma. Daga lokacin har zuwa shekarar 1945, sojoji ‘yan Afirka sun yi ta kokarin yaki da sojojin Japan a Burma. Inda bajintar da wadannan sojojin Afirka suka nuna a yaki ta bar ma makiya mamaki matuka.

 

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

A lokacin kasar Sin ba ta tsaya kan tinkarar mahara Japanawa a ciki gidanta kadai ba, har ma bisa bukatar Birtaniyya, ta tura sojoji zuwa kasar Burma don tallafawa yakin da ake yi da sojojin Japan a can. Daga watan Oktoba na 1943 zuwa na Maris na 1945, sojojin kasar Sin sun hallaka sojojin Japan sama da 49,000, tare da kwato garuruwa da Japanawa suka mamaye sama da 50 a arewacin Burma. Sojojin kasar Sin sun kuma yi asara sosai, inda yawan mutanensu da suka rasa rai ko kuma suka ji rauni ya kai sama da 60,000.

 

Gudunmawar da magabata suka bayar, abu ne da ya kamata a tuna da shi. Mun san daga baya, tsoffin sojojin Afirka a yakin duniya na biyu sun taka muhimmiyar rawa a gwagwarmayar neman ‘yancin kai na kasashen Afirka, yayin da Sin ma ta tabbatar da matsayinta a idanun mutanen duniya, ta hanyar bayar da gagarumar gudummawa wajen yaki da ‘yan Fascist a duniya.

 

Kuma domin tunawa da tarihi ne, a jiya (15 ga watan Agusta, wato ranar cikar shekaru 80 da kasar Japan ta mika wuya ba tare da wani sharadi ba ga kawancen yaki da ‘yan Fascist), na ziyarci gidan tarihi na tunawa da yakin kin harin Japan da jama’ar kasar Sin suka yi, da ke birnin Beijing na Sin, domin maimaita tarihin yadda jama’ar kasar Sin suka yi tsayin daka wajen adawa da zaluncin mahara Japanawa. Ta hanyar kallon abubuwan da aka adana, da hotuna, da bidiyo, da rubutaccen bayanin da aka nuna, na sake gane wa idona irin ta’asar da mahara Japanawa suka aikata: kisan kiyashin da aka yi wa mutane kimanin 300,000 a Nanjing, babban birnin kasar Sin a lokacin; da yadda rundunar 731 ta kasar Japan ta gudanar da gwaje-gwajen kai tsaye kan jama’ar kasar Sin masu rai, don bincike da kera makaman kare dangi masu guba; da yadda sojojin Japan suka yi kokarin tabbatar da ganin a kona dukkan gidaje, da kashe dukkan mutane, da kuma kwace dukkan dukiyoyi, a dimbin kauyuka marasa adadi na kasar Sin. A sa’i daya kuma, na ji irin ruhin da jama’ar kasar Sin suke da shi na hakuri da jure wahalhalu, da yadda suke matukar kokari wajen tabbatar da samun nasara a yakin kin harin Japan. A yakin da aka kwashe shekaru 14 ana yinsa, kasar Sin ta samu asarar sojoji da fararen hula (mutuwa ko jin rauni) sama da miliyan 35, wato adadin kusan kashi daya bisa uku na jimillar wadanda suka mutu ko suka ji rauni a yakin duniya na biyu a fadin duniya.

 

Har ila yau, a zamanin da muke ciki, tunawa da tarihi yana da ma’anar musamman:

Ta hanyar tunawa da tarihi, muna dakile yunkurin mutanen da suke kokarin boye gaskiya, inda za mu tunatar da su cewa kisan kiyashi na Nanjing, da ta’asar da rundunar 731 ta aikata, abubuwa ne na gaske da suka taba faruwa, wadanda ba za a iya goge su daga cikin tarihi ba, kuma kasar Japan ba za ta iya tserewa alhakin laifukan cin zarafin bil’adama ba; kana za mu bayyana karara cewa, komawar yankin Taiwan zuwa cikin harabar kasar Sin yana daga cikin sakamakon da aka samu a yakin kin ‘yan Fascist a duniya, wadda ba za a iya gyara ta ba.

Haka zalika, tunawa da tarihi yana ba mu damar gadon ruhin hadin kai da gwagwarmaya. Jama’a daga ko’ina cikin duniya, ciki har da Afirka da Sin, sun taba yin hadin gwiwa karkashin tutar adalci, inda suka yi fafutuka kafada da kafada, don tabbatar da makoma mai haske ta bil’adama. Wannan ruhin yanzu an mai da shi ya zama niyyar gina “al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya,” wadda ta sanya mu yin aiki tare don samun zaman lafiya a duniya, da ci gaban bai daya a tsakanin dukkanin kasashe.

 

Tunawa da tabbatar da tarihi za su karfafa imaninmu kan cewar, wadanda ke neman yin kashin dankali a duniya ba za su samu biyan bukata ba, kuma nasara ta karshe za ta kasance ta mutane, da kasashe masu ra’ayin daukaka zaman lafiya da tabbatar da yanayin adalci a duniya. (Bello Wang)

Tarihi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • Sulaiman
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

Matsalar Gishiri Ga Lafiyar Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.