• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Aka Kasa Shawo Kan Matsalar Hare-haren Bindiga A Kasar Amurka?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya da dare,aka samu harin bindiga a jami’ar Morgan da ke jihar Maryland ta kasar Amurka, harin da ya jikkata wasu mutane biyar. 

Hakika, hare-haren bindiga na kara addabar yara da matasa a kasar Amurka. Alkaluman da cibiyar rigakafi da shawo kan cututtuka ta kasar Amurka ta samar a kwanan baya sun yi nuni da cewa, hare-haren bindiga sun zarce hadurran mota har sun zo na farko a matsayin dalilin mutuwar yara da matasa a kasar.

  • An Yabawa Ci Gaban Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin Yayin Liyafar Da Aka Shirya Domin Murnar Cikarta Shekaru 74 Da Kafuwa 
  • Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Alkaluman sun shaida cewa, daga shekarar 2019 zuwa ta 2021, yara da matasan da suka halaka sakamakon hare-haren bindiga sun karu da kaso 50%, ko a shekarar 2021 kadai, kimanin kaso 19% na mutuwar yara da matasa na da alaka da hare-haren bindiga.

Lamarin da ya sa na tuna da wani hoton bidiyon da aka watsa ta yanar gizo a bara, wanda ya janyo cece-kuce daga masu kallonsa. Bidiyon ya nuna yadda wata ‘yar Amurka ta sayo wa danta mai shekaru 5 da haihuwa wata jakar karatu da za ta iya kare shi daga harbin bindiga, tare da horar da shi a gida kan yadda zai iya gudu daga hare-haren bindiga. Wadanda suka kalli bidiyon da dama sun ce, hakan abin bakin ciki ne. Babu shakka, sai dai gaskiyar lamarin da ya faru ya fi hakan bakanta wa mutane rai, alkaluman da cibiyar kididdigar harkokin ba da ilmi ta kasar Amurka(NCES) ta samar sun yi nuni da cewa, daga shekarar 2021 zuwa ta 2022, gaba daya an samu lamuran harbe-harben bindiga 327 a makarantun kasar, ciki har da na firamare da na sakandare, kuma 188 daga cikinsu sun haifar da mutuwar mutane ko jikkatarsu.

Hare-haren bindiga da ake ta samu a kasar ya sa al’ummar kasar ke ta kira ga gwamnati da ta dauki matakai na shawo kan matsalar, sai dai sakamakon yadda jam’iyyun siyasar kasar suke ta ja-in-ja da juna, da ma yadda masu kera bindigogi da ‘yan siyasa na kasar suke hada baki da juna, ya sa da wuya gwamnatin kasar ta fitar da ingantattun matakai da za su kai ga shawo kan matsalar.

Labarai Masu Nasaba

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Yara manyan gobe, abin kunya ne yadda kasar ta Amurka ta kasa kare yaranta daga hare-haren bindiga. Rayuka su ne tushen hakkin dan Adam, kuma abin takaici ne yadda hare-haren bindiga suke ta halaka ’yan kasar. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaDaukar Nauyin Ta'addanciHare-haren bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Maraba Da Ziyarar Sanatocin Amurka

Next Post

Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

Related

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

10 minutes ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

3 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

5 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

6 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

17 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

21 hours ago
Next Post
Kefas

Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.