• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ke Goyon Bayan Matakin Japan Na Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku?

by CMG Hausa
2 years ago
Amurka

A daidai lokacin da kasashen duniya ke yin Allah wadai da yadda gwamnatin kasar Japan ta kare aniyarta ta zubar da ruwan dagwalon nukiliya na tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku, jakadan kasar Amurka a Japan Rahm Emanuel ya yi tattaki zuwa Fukushima, inda ya nuna yadda ya ci abincin teku na wurin, don bayyana goyon baya ga matakin da Japan ta dauka na zubar da ruwan cikin teku. Amma da gaske ne Amurka ba ta damu da illolin da matakin na Japan ka iya haifarwa? 

Alkaluman da ma’aikatar kula da aikin gona da dazuzzuka da albarkatun ruwa ta kasar Japan ta fitar sun shaida cewa, Amurka ta kasance kasar da ta fi yawan rage shigowa da kayayyakin ruwa daga kasar Japan tun farkon bana, musamman ma wasu nau’o’in abincin teku da suka fito daga yankin da ruwan dagwalon nukiliya ya fi shafa. Da haka, muna iya gano cewa, gwamnatin Amurka na sane da illolin da matakin ka iya haifarwa. To, ke nan me ya sa Amurka ta nuna hakuri har ma ta goyi bayan Japan ?

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani

A hakika, matsayin da Amurka ke dauka kamar ciniki ne take yi da Japan, inda ta hanyar bayyana goyon baya da fahimta, Amurka ke taimakawa Japan wajen tinkarar kyama da shakku da ake nuna mata, yayin da Japan a nata bangare, ta kara ba Amurka hadin kai wajen aiwatar da shirye-shiryenta a duniya. A hakika, a cikin shekaru biyu da suka wuce, Japan ta yi ta kokarin ba da hadin kai wajen aiwatar da tsarin tattalin arziki a kasashen dake yankin tekun Indiya da fasifik wato Indo-Pacific da Amurka ke jagoranta.

Amurka wadda a kullum ke ikirarin mai rajin kare muhalli, amma ainihin abin da take kulawa ba muhallin duniya ba ne, illa ci gaba da yin babakere a duniya.

Makonni biyu ke nan da Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, kuma hakan zai ci gaba nan da shekaru 30 zuwa 40 masu zuwa. Wani nazarin da jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi ya shaida cewa, da farkon fari, kasashen da ke yammacin tekun Pasifik ne za su fi fuskantar illolin da matakin zai haifar, amma sakamakon igiyar ruwa, nan da shekaru 10 masu zuwa, yankin Amurka da ke gabashin tekun za su fuskanci tarin sinadarai masu guba da suka ninka na mashigin teku na Japan har sau uku.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

Abin takaici shi ne, ‘yan siyasa na Amurka sun fi mai da hankali a kan cimma moriyarsu ta yanzu, babu ruwansu da matsaloli da gwamnati ta gaba za ta fuskanta. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Next Post
Zamfara

Dusa Muke Ci Muke Rayuwa Saboda Tsananin Rashin Tsaro - Mazauna Wani Yankin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.