ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ke Goyon Bayan Matakin Japan Na Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku?

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A daidai lokacin da kasashen duniya ke yin Allah wadai da yadda gwamnatin kasar Japan ta kare aniyarta ta zubar da ruwan dagwalon nukiliya na tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku, jakadan kasar Amurka a Japan Rahm Emanuel ya yi tattaki zuwa Fukushima, inda ya nuna yadda ya ci abincin teku na wurin, don bayyana goyon baya ga matakin da Japan ta dauka na zubar da ruwan cikin teku. Amma da gaske ne Amurka ba ta damu da illolin da matakin na Japan ka iya haifarwa? 

Alkaluman da ma’aikatar kula da aikin gona da dazuzzuka da albarkatun ruwa ta kasar Japan ta fitar sun shaida cewa, Amurka ta kasance kasar da ta fi yawan rage shigowa da kayayyakin ruwa daga kasar Japan tun farkon bana, musamman ma wasu nau’o’in abincin teku da suka fito daga yankin da ruwan dagwalon nukiliya ya fi shafa. Da haka, muna iya gano cewa, gwamnatin Amurka na sane da illolin da matakin ka iya haifarwa. To, ke nan me ya sa Amurka ta nuna hakuri har ma ta goyi bayan Japan ?

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani

A hakika, matsayin da Amurka ke dauka kamar ciniki ne take yi da Japan, inda ta hanyar bayyana goyon baya da fahimta, Amurka ke taimakawa Japan wajen tinkarar kyama da shakku da ake nuna mata, yayin da Japan a nata bangare, ta kara ba Amurka hadin kai wajen aiwatar da shirye-shiryenta a duniya. A hakika, a cikin shekaru biyu da suka wuce, Japan ta yi ta kokarin ba da hadin kai wajen aiwatar da tsarin tattalin arziki a kasashen dake yankin tekun Indiya da fasifik wato Indo-Pacific da Amurka ke jagoranta.

ADVERTISEMENT

Amurka wadda a kullum ke ikirarin mai rajin kare muhalli, amma ainihin abin da take kulawa ba muhallin duniya ba ne, illa ci gaba da yin babakere a duniya.

Makonni biyu ke nan da Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, kuma hakan zai ci gaba nan da shekaru 30 zuwa 40 masu zuwa. Wani nazarin da jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi ya shaida cewa, da farkon fari, kasashen da ke yammacin tekun Pasifik ne za su fi fuskantar illolin da matakin zai haifar, amma sakamakon igiyar ruwa, nan da shekaru 10 masu zuwa, yankin Amurka da ke gabashin tekun za su fuskanci tarin sinadarai masu guba da suka ninka na mashigin teku na Japan har sau uku.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Abin takaici shi ne, ‘yan siyasa na Amurka sun fi mai da hankali a kan cimma moriyarsu ta yanzu, babu ruwansu da matsaloli da gwamnati ta gaba za ta fuskanta. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Zamfara

Dusa Muke Ci Muke Rayuwa Saboda Tsananin Rashin Tsaro - Mazauna Wani Yankin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.