ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Amurka Ke Goyon Bayan Matakin Japan Na Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku?

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A daidai lokacin da kasashen duniya ke yin Allah wadai da yadda gwamnatin kasar Japan ta kare aniyarta ta zubar da ruwan dagwalon nukiliya na tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku, jakadan kasar Amurka a Japan Rahm Emanuel ya yi tattaki zuwa Fukushima, inda ya nuna yadda ya ci abincin teku na wurin, don bayyana goyon baya ga matakin da Japan ta dauka na zubar da ruwan cikin teku. Amma da gaske ne Amurka ba ta damu da illolin da matakin na Japan ka iya haifarwa? 

Alkaluman da ma’aikatar kula da aikin gona da dazuzzuka da albarkatun ruwa ta kasar Japan ta fitar sun shaida cewa, Amurka ta kasance kasar da ta fi yawan rage shigowa da kayayyakin ruwa daga kasar Japan tun farkon bana, musamman ma wasu nau’o’in abincin teku da suka fito daga yankin da ruwan dagwalon nukiliya ya fi shafa. Da haka, muna iya gano cewa, gwamnatin Amurka na sane da illolin da matakin ka iya haifarwa. To, ke nan me ya sa Amurka ta nuna hakuri har ma ta goyi bayan Japan ?

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani

A hakika, matsayin da Amurka ke dauka kamar ciniki ne take yi da Japan, inda ta hanyar bayyana goyon baya da fahimta, Amurka ke taimakawa Japan wajen tinkarar kyama da shakku da ake nuna mata, yayin da Japan a nata bangare, ta kara ba Amurka hadin kai wajen aiwatar da shirye-shiryenta a duniya. A hakika, a cikin shekaru biyu da suka wuce, Japan ta yi ta kokarin ba da hadin kai wajen aiwatar da tsarin tattalin arziki a kasashen dake yankin tekun Indiya da fasifik wato Indo-Pacific da Amurka ke jagoranta.

ADVERTISEMENT

Amurka wadda a kullum ke ikirarin mai rajin kare muhalli, amma ainihin abin da take kulawa ba muhallin duniya ba ne, illa ci gaba da yin babakere a duniya.

Makonni biyu ke nan da Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, kuma hakan zai ci gaba nan da shekaru 30 zuwa 40 masu zuwa. Wani nazarin da jami’ar Tsinghua ta kasar Sin ta yi ya shaida cewa, da farkon fari, kasashen da ke yammacin tekun Pasifik ne za su fi fuskantar illolin da matakin zai haifar, amma sakamakon igiyar ruwa, nan da shekaru 10 masu zuwa, yankin Amurka da ke gabashin tekun za su fuskanci tarin sinadarai masu guba da suka ninka na mashigin teku na Japan har sau uku.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Abin takaici shi ne, ‘yan siyasa na Amurka sun fi mai da hankali a kan cimma moriyarsu ta yanzu, babu ruwansu da matsaloli da gwamnati ta gaba za ta fuskanta. (Mai zane: Mustapha Bulama)

 

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Zamfara

Dusa Muke Ci Muke Rayuwa Saboda Tsananin Rashin Tsaro - Mazauna Wani Yankin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.