• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Me ya sa kasar Sin ba za ta bar Taiwan samun ‘yancin kai ba?” Wani ma’aikacin banki ya yi mana wannan tambaya, yayin da nake kula da wasu ayyuka a wani banki dake Lagos na Najeriya, wasu shekaru da suka wuce. Sa’an nan, na mayar masa da wata tambaya ta daban, wato “Me ya sa tarayyar Najeriya ba ta ba Biafra damar samun ‘yancin kanta ba?”

Da ma’aikacin ya ji wannan tambayar, sai ya yi murmurshi, ya kuma cewa abokin aikinsa, “Ga wannan mutum da ya san tarihinmu.”

  • Ko Barcelona Ta Kama Hanyar Lashe Gasar Laliga Ta Bana?
  • Yunkurin Neman ‘Yancin Kan Taiwan Ya Shaida Yunkurin Lai Ching-te Na Neman Mulki Irin Na Kama Karya Ta Hanyar Demokuradiyya

Duk wani lokaci da wani aboki ya tambaye ni kan batun Taiwan, na kan gaya masa cewa, idan mun bayyana batun bisa wani tsari a takaice, to, yankin Taiwan ga kasar Sin, tamkar yankin kudu maso gabashin Najeriya a karkashin ikon Biafra ga tarayyar Najeriya. Najeriya ta jure yakin basasa na shekaru 3, da mutuwar mutane kimanin miliyan 1, wajen hana ballewar yankin kudu maso gabas. Hakazalika kasar Sin ita ma a nata bangare, tana da irin wannan niyya mai karfi, don tabbatar da dinkuwar kasa.

Ko da yake sanin tushen batun Taiwan ba shi da sarkakiya, amma a kan iya ganin kuskure cikin bayanan da kafofin watsa labaru na Najeriya suka gabatar dangane da batun. Misali, a kwanan baya, jaridar Premium Times ta ruwaito maganar da Andy Yih-Ping Liu, shugaban ofishin harkar ciniki na Taipei, ya fada, inda ya zargi gwamnatin Najeriya da “bin umarnin kasar Sin”, bisa bukatar hukumar Taiwan da ta janye ofishinta daga birnin Abuja zuwa Lagos, da sake nada masa suna “ofishin harkar ciniki na Taipei”. Sai dai maganar gaskiya ita ce, manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, (wadda ta kunshi bangarori uku: 1. Akwai kasar Sin daya tak a duniya. 2. Taiwan wani yanki na kasar Sin ne da ba za a iya balle shi daga kasar ba. 3. Gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin ita ce halastacciyar gwamnati daya tak dake wakiltar daukacin yankunan kasar Sin.) ita ce tushen kulla huldar diplomasiyya da kasar Sin. Saboda haka, yadda Najeriya take da huldar diplomasiyya da kasar Sin, ya nuna yadda kasar take yarda da manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. To, hakan zai hana gwamnatin Najeriya baiwa yankin Taiwan damar kafa ofishi a Abuja, wadda take ba wa kasashe masu ‘yancin kai kawai. Ta haka ma za a fahimta cewa, matakin da Najeriya ta dauka cika alkawari ne, maimakon bin umarnin wani.

Ban da haka, a cikin bayanin jaridar Premium Times, an ce “Bayan da aka kawo karshen yakin basasa a kasar Sin a shekarar 1949, jam’iyyar KMT ta tsira zuwa Taiwan, inda ta kafa jamhuriyar kasar Sin.” To, wannan maganar ita ma ba haka take ba. Maganar gaskiya ita ce, an kafa jamhuriyar kasar Sin tun shekarar 1912, wadda ta kunshi harabar babban yankin kasar Sin, da ta yankin Taiwan, na yanzu. Sa’an nan a sakamakon kammalar yakin basasa a shekarar 1949, gwamnatin tsakiya na jamhuriyar jama’ar kasar Sin ta kafu, wadda ta maye gurbin gwamnatin jamhuriyar kasar Sin a matsayin halastacciyar gwamnati daya tak ta daukacin yankunan kasar Sin, da halastacciyar wakiliya ta kasar Sin guda daya tak a duniya. Lamarin da ya kawo karshen jamhuriyar kasar Sin a lokacin.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

Sai dai hukumar yankin Taiwan na ci gaba da kokarin yada karairayi, tare da tunasar da kowa kasancewarta. In ba haka ba, wadannan bayanai masu kunshe da kurakurai da muka ambata ba za su bayyana a kan wata jaridar Najeriya ba. Hakika, a shekarun nan, hukumar Taiwan ta yi ta kokarin takala da batun neman “‘yancin kan Taiwan”, lamarin da ya haifar da mummunar barazana ga zaman lafiyar shiyyar da yankin ke ciki. Kamar ba su cika lura da dokar kin barakar kasa ta kasar Sin, wadda aka fara aiwatar da ita wasu shekaru 20 da suka wuce ba. Sai dai an tanada a cikin dokar da cewa, babban yankin kasar Sin zai nuna cikakken sahihanci, da iyakacin kokarin tabbatar da dinkuwar kasa ta hanyar lumana, amma zai dauki kwararran matakan da suka wajaba, idan masu neman “‘yancin kan Taiwan” sun wuce gona da iri.

Tabbas za a tabbatar da dinkuwar kasar Sin waje guda. Yadda masu neman balle yankin Taiwan ke ta da zaune-tsaye ba zai haifar musu da da mai ido ba, illa sanya su gamuwa da ajalinsu cikin sauri. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaba Tinubu

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Umarci Ma’aikatanta Da Su Tantance Allbashin Watan Maris Kafin A Biya Su

Related

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

3 days ago
Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

1 week ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

2 weeks ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

2 weeks ago
Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
Ra'ayi Riga

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

2 weeks ago
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
Ra'ayi Riga

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

2 weeks ago
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Umarci Ma’aikatanta Da Su Tantance Allbashin Watan Maris Kafin A Biya Su

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.