• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Kasashen BRICS na kasance tamkar maganadiso, wanda ke ta jawo masu neman tabbatar da zaman lafiya da hadin gwiwa… Mu ma Venezuala, muna fatan zama daya daga cikin kasashe mambobin BRICS.”

Shugaban kasar ta Venezuala Nicolás Maduro Moros ne ya fadi haka a kwanan baya a gun taron manema labarai da aka shirya bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Brazil.

  • Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

Daga ranar 1 zuwa 2 ga wata, an gudanar da taron ministocin wajen kasashen BRICS a birnin Cape Town na kasar Afirka ta kudu, kuma fadada mambobin kungiyar na daya daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a gun taron.

Bayanai na cewa, kasashe da dama ciki har da kasashen Afirka irinsu Aljeriya da Masar, duk sun bayyana burinsu na zama mambobin kungiyar BRICS, kafin wannan kuma, wakilin musamman na gwamnatin kasar Afirka ta kudu mai kula da harkokin Asiya da gabas ta tsakiya da kuma kasashen BRICS, Anil Sooklal ya bayyana cewa, “Kusan muna samun sakwannin neman zama mambar BRICS a kowace rana.”
Amma me ya sa BRICS ke kara farin jini?
In mun yi nazari, za mu gano cewa, hakan ya faru ne sabo da na farko, kungiyar BRICS na jawo hankalinsu ne sabo da yadda take neman hadin gwiwa da ci gaba, a maimakon rarrabuwar kawuna da yin fito na fito da juna.

Ba kamar yadda Amurka da kawayenta na yammacin duniya su kan kulla kawance ne don su tinkari wani, tsarin BRICS tun farkon kafuwarsa yana mai da hankali ne a kan inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa. A sa’i daya kuma, ba ya da niyyar yin fito na fito da kasashen yamma ko kuma maye gurbinsu.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Na biyu kuma, kasashen BRICS na dukufa a kan daidaita tsarin gudanar da harkokin duniya da ma kiyaye moriyar kasashe masu tasowa, sakamakon yadda kasashe masu tasowa ke fuskantar karancin wakilci da ma jin muryarsu a harkokin duniya. Tun kafa shi, tsarin na BRICS ya yi ta kokarin fito da muryar kasashe masu tasowa a duniya da kuma kare moriyarsu ta bai daya.

In mun dauki misali da asusun ba da lamuni na duniya(IMF), wanda kasancewarsa muhimmiyar hukumar kula da hada-hadar kudi ta duniya, amma kuma ta dade tana wakiltar kasashen yamma ne kawai.

Sai dai bisa kwaskwarima da aka sha yiwa asusun, tsarin BRICS ya kyautata wakilcin kasashe da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa a hukumar ta IMF.

A gun taron ministocin wajen BRICS da aka gudanar a wannan karo kuma, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Ma Zhaoxu ma ya sake jaddada cewa, ya kamata a kara wakilcin kasashe masu tasowa tare da kara jin muryarsu a harkokin duniya.

Na uku, BRICS na mai da hankali ne a kan cimma hakikanan nasarori da za su amfanawa kasashe masu tasowa.

In mun dauki misali da bankin NDB da kasashen BRICS suka kafa, wanda ya kasance banki na tsakanin kasa da kasa na farko da kasashe masu tasowa suka kafa, wanda tun kafuwarsa a shekaru 7 da suka wuce har zuwa yanzu, rancen kudin da ya samar har ya kai dala biliyan 32, wanda aka zuba su a fannonin bunkasa ababen more rayuwa da ma wasu ayyuka na tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen BRICS.

Musamman ma a lokacin da aka fuskanci annobar Covid-19, Bankin ya samar da kudin agajin gaggawa na dala biliyan 10 ga kasashe mambobin BRICS.

Yadda karin kasashe ke neman zama mambobin BRICS ya shaida mana bukatu na bai daya na kasashe masu tasowa, wato yin hadin gwiwa da juna don tabbatar da bunkasuwar juna, da kara tabbatar da adalcin tsarin duniya.(Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sana’ar Kwalliya

Next Post

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

15 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

16 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

17 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

18 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

19 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

21 hours ago
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.