ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

“Kasashen BRICS na kasance tamkar maganadiso, wanda ke ta jawo masu neman tabbatar da zaman lafiya da hadin gwiwa… Mu ma Venezuala, muna fatan zama daya daga cikin kasashe mambobin BRICS.”

Shugaban kasar ta Venezuala Nicolás Maduro Moros ne ya fadi haka a kwanan baya a gun taron manema labarai da aka shirya bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Brazil.

  • Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

Daga ranar 1 zuwa 2 ga wata, an gudanar da taron ministocin wajen kasashen BRICS a birnin Cape Town na kasar Afirka ta kudu, kuma fadada mambobin kungiyar na daya daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a gun taron.

ADVERTISEMENT

Bayanai na cewa, kasashe da dama ciki har da kasashen Afirka irinsu Aljeriya da Masar, duk sun bayyana burinsu na zama mambobin kungiyar BRICS, kafin wannan kuma, wakilin musamman na gwamnatin kasar Afirka ta kudu mai kula da harkokin Asiya da gabas ta tsakiya da kuma kasashen BRICS, Anil Sooklal ya bayyana cewa, “Kusan muna samun sakwannin neman zama mambar BRICS a kowace rana.”
Amma me ya sa BRICS ke kara farin jini?
In mun yi nazari, za mu gano cewa, hakan ya faru ne sabo da na farko, kungiyar BRICS na jawo hankalinsu ne sabo da yadda take neman hadin gwiwa da ci gaba, a maimakon rarrabuwar kawuna da yin fito na fito da juna.

Ba kamar yadda Amurka da kawayenta na yammacin duniya su kan kulla kawance ne don su tinkari wani, tsarin BRICS tun farkon kafuwarsa yana mai da hankali ne a kan inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa. A sa’i daya kuma, ba ya da niyyar yin fito na fito da kasashen yamma ko kuma maye gurbinsu.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Na biyu kuma, kasashen BRICS na dukufa a kan daidaita tsarin gudanar da harkokin duniya da ma kiyaye moriyar kasashe masu tasowa, sakamakon yadda kasashe masu tasowa ke fuskantar karancin wakilci da ma jin muryarsu a harkokin duniya. Tun kafa shi, tsarin na BRICS ya yi ta kokarin fito da muryar kasashe masu tasowa a duniya da kuma kare moriyarsu ta bai daya.

In mun dauki misali da asusun ba da lamuni na duniya(IMF), wanda kasancewarsa muhimmiyar hukumar kula da hada-hadar kudi ta duniya, amma kuma ta dade tana wakiltar kasashen yamma ne kawai.

Sai dai bisa kwaskwarima da aka sha yiwa asusun, tsarin BRICS ya kyautata wakilcin kasashe da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa a hukumar ta IMF.

A gun taron ministocin wajen BRICS da aka gudanar a wannan karo kuma, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Ma Zhaoxu ma ya sake jaddada cewa, ya kamata a kara wakilcin kasashe masu tasowa tare da kara jin muryarsu a harkokin duniya.

Na uku, BRICS na mai da hankali ne a kan cimma hakikanan nasarori da za su amfanawa kasashe masu tasowa.

In mun dauki misali da bankin NDB da kasashen BRICS suka kafa, wanda ya kasance banki na tsakanin kasa da kasa na farko da kasashe masu tasowa suka kafa, wanda tun kafuwarsa a shekaru 7 da suka wuce har zuwa yanzu, rancen kudin da ya samar har ya kai dala biliyan 32, wanda aka zuba su a fannonin bunkasa ababen more rayuwa da ma wasu ayyuka na tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen BRICS.

Musamman ma a lokacin da aka fuskanci annobar Covid-19, Bankin ya samar da kudin agajin gaggawa na dala biliyan 10 ga kasashe mambobin BRICS.

Yadda karin kasashe ke neman zama mambobin BRICS ya shaida mana bukatu na bai daya na kasashe masu tasowa, wato yin hadin gwiwa da juna don tabbatar da bunkasuwar juna, da kara tabbatar da adalcin tsarin duniya.(Lubabatu Lei)

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.