• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
FOCAC

Tun daga farkon wannan mako, Beijing, babban birnin kasar Sin ya fara karbar baki daga kasashen Afrika da suka hada da shugabannin kasashe da gwamnatoci da ma manyan jami’ai, da suka zo domin halartar taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afrika wato FOCAC. A bana, Beijing zai sake ganin haduwar shugabannin bangarorin biyu, bayan wanda aka yi a shekarar 2018. 

 

Dandalin FOCAC dai ya zama wata laima da hadin gwiwar Sin da Afrika ke fadada karkashinsa, duba da irin alfanun da yake tattare da shi. Tun bayan kafuwarsa shekaru 25 da suka gabata, har kullum dandalin na nacewa ne ga ka’idojin gudanar da tsare-tsare tare, samun ci gaba tare da ma moriyar juna tsakanin bangarorin biyu.

  • An Gudanar Da Taron Ministoci Na Dandalin FOCAC Karo Na 9 A Beijing
  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Me ya sa dandalin da ma dangantakar Sin da Afrika ke samun karbuwa?

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

A duk lokacin da aka ambaci kasar Sin, ba shakka abun da zai zo ran al’ummar Afrika shi ne, taimakon kasar gare su. Tabbas kasar Sin ta zama aminiya ta kwarai mai taimako ba tare da la’akari da ana cikin wuya ko dadi ba, kana ba tare da wani sharadi ko yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashen Afrika ba. Taimakon kasar Sin ya isa lungu da sako da kowanne bangare na Afrika. Kama daga ababen more rayuwa zuwa kiwon lafiya da tallafin ilimi da cinikayya da horo da abinci da sauransu.

 

Na yi imani a cikin lokacin da aka dauka ana hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, ta samar da taimako na zahiri da manyan kasashe masu mulkin mallaka ba su samar ba, tsawon lokacin da suka dauka suna mamaya a nahiyar Afrika.

 

Hausawa kan ce, ruwan da ya dauke ka, shi ne ruwa. Ina da yakinin babu wani mutum daga nahiyar Afrika da bai ci moriyar wani abu daga kasar Sin ba. Jama’ar Afrika, sun gani kuma sun shaida huldar Sin da kasashensu, sun kuma ga alfanunta a zahiri, shi ya sa kasar Sin ke kara samun karbuwa a wajensu. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki
Daga Birnin Sin

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
Next Post
Kasashen Yamma Na Yunkurin Cimma Burinsu Ta Hanyar Goyon Bayan Philiphines

Kasashen Yamma Na Yunkurin Cimma Burinsu Ta Hanyar Goyon Bayan Philiphines

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.