• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Baki sama da 300 daga Sin da kasashen Afrika 53 ne suka tattauna a jiya Litinin game da gudanar da taron dandalin FOCAC na badi.  

Dandalin FOCAC dai ya kasance muhimmiyar laima da kasashen Sin da Afrika ke hadin gwiwa karkashinta, wanda kuma ke samun karbuwa matuka tsakanin kasashen Afrika. Shin me ya sa dangantaka da Sin ke kara samun karbuwa a Afrika?

  • Sin Na Fatan Za’a Daidaita Batun Palestinu Daga Dukkan Fannoni Kuma Na Dogon Lokaci
  • Bikin Ranar Majalisar Dinkin Duniya: Muna Fuskantar Kalubalen Da Ba A Taba Ganin Irinsa Ba – Schmale

Saboda kasar Sin ta zo da sabuwar dabarar hadin gwiwa da ba a saba gani ba. Wato mutuntawa da girmawawa da moriyar juna. A baya, hadin gwiwa da kasashen Afrika ke yi da iyayen gidansu, ta kasnace bisa wasu sharudda da wadancan kasashe ke gindayawa ko kuma ci da gumin kasashen da kwashe albarkatunsu. Amma a yanzu, ba haka abun yake ba, kasashen Afrika sun san darajar kansu saboda yadda kasar Sin ke daukarsu a matsayin ’yan uwanta ba tare da nuna iko ko fifiko ba.

Abu na biyu shi ne, kasar Sin tana fada da cikawa. Wato tana samar da tarin damarmaki tare da cika alkawuranta. Na yi imanin cewa, irin alfanun da kasashen suka samu daga hadin gwiwarsu da Sin a kankanin lokaci, bai kai abun da suka samu daga iyayen gidansu masu mulkin mallaka ba. Babu inda kasar Sin ba ta taba ba a fannonin rayuwar al’umma, kama daga ababen more rayuwa zuwa tsaro da kasuwanci da fasahohi da sauransu. Ba za a iya taba raba ci gaban da kasashen Afrika suka samu cikin sauri ba da taimakon kasar Sin.

Abu na 3 a ganina shi ne, yadda kasar Sin ta samarwa kasashen Afrika damar bayyana ra’ayinsu. Bisa yadda take tafiyar da dangantakarta da su, yanzu kasashen Afrika sun san abun da ya dace da su, da yadda za su kwaci kansu. Yayin wani taro da aka gudanar tsakanin kasashen Afrika da na Turai a kwanakin baya, na ji shugaban wata kasa a Afrika na cewa, lallai ya kamata a rika daukarsu da muhimmanci. Kuma kamata ya yi a rika ba su dama kamar sauran manyan kasashe. Wannan tamkar nanata kira da kokarin da kasar Sin ne na ganin duniya ba ta kasance karkashin ikon wata kasa ko wasu tsiraru ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Hakika kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kai da ci gaban kasashen Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FOCACSin da Afirkaziri daya
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Kashe Dalibar Kwaleji A Gombe

Next Post

Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

56 minutes ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

2 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

3 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

4 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

23 hours ago
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

24 hours ago
Next Post
Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.