• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Erik Ten Hag Yake Goyon Bayan Harry Maguire? 

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Harry Maguire

Dan wasa Harry Maguire dai yana ci gaba da fuskantar suka daga bangarori da daman a magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Manchester United da kuma na tawagar kasar Ingila sakamakon rashin kokarinsa.

Sai dai mai koyar da ‘yan wasan kungiyar Manchester United Erik ten Hag ya ce ya yarda da kwallon kyaftin din kungiyar Harry Maguire duk da sukar da ake yi wa dan kwallon saboda rashin tabuka komai.

  • Wakilin Sin Ya Yi Cikakken Bayani Kan Sakamakon Da Jihar Xinjiang Ta Samu Wajen Kare Hakkin Bil Adam
  • Duba Ga Dokokin Da Samari Ke Kakaba Wa ‘Yan Matan Da Za Su Aura

Maguire na shan suka daga magoya bayan kungiyar tare da magoya bayan kasarsa bayan kuskuren da ya tafka a wasansu da Jamus a wasan da suka yi 3-3 a gasar cin kofin Nations League.

“Ina kare shi saboda na yarda kuma na amince da shi kuma maganar dai a kan shi ce, kuma na yi imani cewa zai iya abin da duk muke bukata, zai dawo kokarinsa kamar yadda yake a baya, ni na yarda da haka” In ji Ten Hag.

Ten Hag ya fi sanya Lisandro Martinez da kuma Raphael barane a matsayin ‘yan bayan sa da yake sanya wa, ya yin da yake bai wa Bruno Fernandez kyaftin a ‘yan makonnin nan kuma wasa uku kacal Maguire ya bugawa Manchester United a wannan kakar.

LABARAI MASU NASABA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Ten Hag ya ci gaba da cewa “Duk da cewa baya cikin ‘yan wasa 11 na farko da ake fara wasa da su amma yana atisaye sosai, Ten Hag ke cewa kan dan wasan me shekara 29 wanda ya koma kungiyar daga Leceister City.

A wannan makon takwaransa na Ingila da Manchester United Luke Shaw yace bai taba ganin irin sukar da ake yi wa Maguire ba a tahirin kwallon kafa ba duk da cewa shima a baya ya sha suka.

Maguire bai buga karawar da Manchester United ta yi ba da abokiyar hamayyarta Manchester City a ranar Lahadi saboda raunin da ya ji kuma ana ganin zai dauki wata daya yana jiyyar ciwon da yaji a tawagar Ingilan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax
Wasanni

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Next Post
Adadin ‘Yancin Mallakar Fasaha Da Suka Samu Amincewa A Sin Ya Kai Miliyan 4.081

Adadin ‘Yancin Mallakar Fasaha Da Suka Samu Amincewa A Sin Ya Kai Miliyan 4.081

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.