• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Gasar Cin Kofin Turai Ta Fi Son Yin Hadin Gwiwa Da Kamfanonin Kasar Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Me Ya Sa Gasar Cin Kofin Turai Ta Fi Son Yin Hadin Gwiwa Da Kamfanonin Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

A halin yanzu, ana gudanar da gasar cin kofin Turai wato UEFA Euro 2024, wadda ke jan hankulan masu sha’awar wasan kwallon kafa na kasa da kasa. A yayin da ake gudanar da irin wannan gasa ta koli, a kan fitar da muhimman labarai na bunkasuwar tattalin arzikin kasashen duniya. A matsayin gasar wasannin kwallon kafa dake kan matsayin koli, wadda aka gudanar bayan annobar cutar COVID-19, gasar cin kofin Turai ta wannan karo tana da manyan iyayen tafiya guda 13, wadanda aka fi sani da abokan hadin gwiwarta na kasashen duniya. Cikin wadannan manyan iyaye tafiya guda 13, akwai na kasar Sin guda 5, hakan ya sa, Sin ta kasance kasar da gasar cin kofin Turai ta fi samun iyayen tafiya cikin gasar ta wannan karo da ma wanda ya gabata.

A gasar bana, iyayen tafiya guda biyar daga kasar Sin sun hada da sana’o’in samar da na’urorin wutar lantarki masu kwakwalwa, da motoci masu aiki da wutar lantarki, da salula masu kwakwalwa, da masu gudanar da harkokin ciniki ta yanar gizo tsakanin kasa da kasa, gami da sana’ar nazarin fasahohin biyan kudi da sauransu. Dukkansu suna sahun gaba cikin sabbin sana’o’in dake samun bunkasuwa da sauri a kasashen duniya.

  • Shugaba Xi Na Kasar Sin Ya Amsa Wasikar Da Mutanen Gundumar Jingning Suka Aika Masa
  • Xi: A Shirya Sin Take Ta Daukaka Dangantakarta Da Poland Zuwa Sabon Matsayi

Cikin ’yan shekarun nan, wasu kamfanonin kasar Sin dake kan gaba a fannoninsu, sun kafa cibiyoyin nazari da masana’antu a kasashen waje, lamarin da ya samar da guraben ayyukan yi ga kasashen da abin ya shafa, tare da ya ba da gudummawar kyautata fasahohinsu. Wadannan kamfanonin suna ci gaba da sabunta kayayyakinsu, yayin da suke kyautata tsarin gudanarwa da ayyukansu, domin samar wa masu sayyaya na kasashen duniya kyawawan kayayyaki da hidimomi masu inganci, kuma masu kare muhalli. Haka kuma, sun shiga kasuwannin duniya, yayin da suke gasa da kamfanonin kasa da kasa cikin yanayin adalci, bisa tunanin bude kofa ga waje.

A halin yanzu, irin babbar gasar dake jan hankulan jama’ar kasashen duniya kamar gasar cin kofin Turai, suna maraba da kamfanonin kasar Sin, ba kawai domin kamfanonin kasar Sin suna da kudi ba, domin suna amincewa da kasar Sin da yadda take yin kwaskwarimar tattalin arziki a cikin gida, domin sa kaimi ga kamfanonin kasar su yi kirkire-kirkire, da kuma ba da jagoranci ga kasashen duniya wajen sabunta fasahohinsu. Kamar yadda wasu masanan tattalin arzikin kasashen duniya suka bayyana, ya kamata iyayen tafiya na irin wannan gasar da take da tasiri ga al’ummomin kasa da kasa, su kasance daga kamfanonin dake iya alamta bunkasuwar tattalin arzikin duniya, da ma wadanda ke yin muhimmin tasiri ga kasashen duniya. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCGTNSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kawar da Shaye-Shayen Tamkar Kawar da Miyagun Laifuka Ne – Kwamandan NDLEA Na Kebbi

Next Post

Ana Ganawa Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

3 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

4 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

5 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

6 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

7 hours ago
Next Post
Ana Ganawa Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya

Ana Ganawa Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.